Home General Babu wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗi – CBN

Babu wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗi – CBN

Babban Bankin Najeriya, CBN ya yi watsi da raɗe-raɗin da wasu ke yaɗawa a ƙasar cewa daga ranar 31 ga watan Disamba mai zuwa za a daina amfani da tsoffin takardun kuɗin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da CBN ɗin ya fitar ranar Alhamis ya ce wannan iƙirari ba gaskiya ba ne kuma ba shi da tushe balle makama.

”Bisa hukuncin ci gaba da amfanin da tsoffin takardun kuɗin da kotun ƙolin Najeriya ta yi a ranar 29 ga watan Nuwamban 2023, ta ce a ci gaba da amfani da takardun ba tare da iyakancewa ba”, in ji sanarwar.

Haka kuma sanarwar ta yi kira ga bankunan ƙasar su ci gaba da mu’amala da tsoffin takardun kuɗin.

Matakin na zuwa ne dai kwana guda da majalisar wakilan ƙasar ta yi kira ga CBN ɗin ya fara shirye-shiryen janye tsoffin takardun kuɗin daga zagayawa.

A shekarar 2022 ne dai tsohuwan gwamnatin Muhammadu Buhari, ta ɓullo da sabbin takardun kuɗin ƙasar na naira 200, da 500 da 1,000, sannan ta bayar da wa’adin daina amfani da tsoffin zuwa ƙarshen shekarar.

Batun ya haifar da ruɗani da tayar da hankali, inda daga baya wasu jihohin ƙasar suka shigar da ƙara a gaban kotun ƙolin ƙasar, wadda kuma ta jinkirta wa’adin, zuwa wani lokaci, inda daga baya ma ta ce a ci gaba da amfani da su ba tare da iyakancewa ba

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp