Home Labarai Kwastam ta kama fatar jaki 180 a jihar Kebbi

Kwastam ta kama fatar jaki 180 a jihar Kebbi

Jami’an hukumar hana fasa kwauri a jihar Kebbi sun sami nasarar kama fatar jaki 180 da ake yunƙurin yin fasa-ƙwaurinta.

Kwamandan rundunar a jihar Kebbi, Iheanacho Ojike, shi ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai.

Ya ce sauran kayaki da suka kwace sun haɗa da litar man fetur har guda 16,300 da tufafi da kuma katan-katan guda 74 na wasu magunduna daban-daban wanda kuɗin fitonsu ya kai sama da naira miliyan 300.

Iheanacho ya ce an yi samu nasarar kama kayan ne bisa irin ƙoƙari da jami’an hukumar suke yi wajen kakkaɓe masu aikata ɓarna.

Kwamandan hukumar ya ce wasu mutane na amfani da lokacin tsadar man fetur wajen safararsa zuwa waje.

Ya ƙara da cewa an kama wasu mutane biyar da ake zargi da hannu a fasa kwaurin kayakin.

Ya kuma gargaɗi masu fasa kwauri da su daina domin jami’ansu a shirye suke wajen cafke su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp