Home General Babu wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗi – CBN

Babu wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗi – CBN

Babban Bankin Najeriya, CBN ya yi watsi da raɗe-raɗin da wasu ke yaɗawa a ƙasar cewa daga ranar 31 ga watan Disamba mai zuwa za a daina amfani da tsoffin takardun kuɗin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da CBN ɗin ya fitar ranar Alhamis ya ce wannan iƙirari ba gaskiya ba ne kuma ba shi da tushe balle makama.

”Bisa hukuncin ci gaba da amfanin da tsoffin takardun kuɗin da kotun ƙolin Najeriya ta yi a ranar 29 ga watan Nuwamban 2023, ta ce a ci gaba da amfani da takardun ba tare da iyakancewa ba”, in ji sanarwar.

Haka kuma sanarwar ta yi kira ga bankunan ƙasar su ci gaba da mu’amala da tsoffin takardun kuɗin.

Matakin na zuwa ne dai kwana guda da majalisar wakilan ƙasar ta yi kira ga CBN ɗin ya fara shirye-shiryen janye tsoffin takardun kuɗin daga zagayawa.

A shekarar 2022 ne dai tsohuwan gwamnatin Muhammadu Buhari, ta ɓullo da sabbin takardun kuɗin ƙasar na naira 200, da 500 da 1,000, sannan ta bayar da wa’adin daina amfani da tsoffin zuwa ƙarshen shekarar.

Batun ya haifar da ruɗani da tayar da hankali, inda daga baya wasu jihohin ƙasar suka shigar da ƙara a gaban kotun ƙolin ƙasar, wadda kuma ta jinkirta wa’adin, zuwa wani lokaci, inda daga baya ma ta ce a ci gaba da amfani da su ba tare da iyakancewa ba

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp