Home General Tinubu ya umarci ministoci da su yi amfani da motoci 3 kacal...

Tinubu ya umarci ministoci da su yi amfani da motoci 3 kacal a tawagarsu

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya taƙaita yawan motocin da ministocinsa da sauran shugabannin hukumomin gwamnati ke amfani da su a tawagarsu zuwa guda uku, inda ya ce ba za a ƙarawa kowa ba.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnatin, Bayo Onanuga ya fitar, shugaba Tinubu ya ce wannan wani mataki daga cikin matakan da gwamnatinsa ke ɗauka na rage kashe kuɗaɗen gwamnati.

Sanarwar ta ce shugaba Tinubu ya kuma bai wa ministocin nasa da shugabannin hukumomi da ka da su yi amfani da masu kare lafiyarsu ko jami’an tsaro da suka wuce biyar, inda kuma ya umarci mai bai wa shugaban shawara kan tsaron ƙasa domin tattaunawa da sojoji da ƴansanda da sauran masu ɗamara kan yadda za a rage yawan jami’an tsaron.

Da ma dai ko a watan Janairu sai da shugaban ya ce ya ɗauki matakan rage kashe kuɗaɗen inda ya rage yawan ƴan tawagarsa yayin bulaguro ƙasar waje daga 50 zuwa 20 sannan shi kuma mataimakin shugaban ƙasa aka bar masa mutum biyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp