Home General Kananan Yara a Jihar Kano na cikin hadarin kamuwa da cutar Polio

Kananan Yara a Jihar Kano na cikin hadarin kamuwa da cutar Polio

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci al’ummar jihar da su tabbatar an yiwa yaran su allurar rigakafin cutar inna wato Polio, domin gujewa yaduwar cutar a cikin al’umma.

Kwamishinan lafiya na jihar Dr. Abubakar labaran Yusuf ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai, a wani bangari na bikin ranar yaki da cutar ta Shan inna a jihar Kano.

Dr. Abubakar labaran ya ce wannan rana na da matukar muhimmancin wajen tunatar da al’ummar yadda wannan cuta ke kassara dan adam da zarar ta shiga jikin sa.

“Mun hadu yau 24 ga watan 10 na  shekarar 2024 domin mu tunatar da kan mu, muhimmancin wannan rana da aka ware musamman saboda cutar shan inna”

“ita wannan cuta, cuta ce wadda kwayar cuta da ake kira “Poliovirus” take janyowa, wadda idan ta shiga jikin dan Adam take janyo nakasu, take bin laka ta jikin dan Adam ta kassarashi, wani ta janyo masa rashin kafa wani rashin hannun, wani ma hannun da kafafuwan su shanye”.

Ya kara da cewa wajibi ne akan ma’aikatan lafiya a jihar kano su tabbatar da an kawar da cutar, daga cikin al’umma domin kaucewa hadarin da take dauke da shi.

“Wannan aiki abu ne mai yiwuwa, kuma za’a iya yin sa, domin ya zama dole akan mu, mu ma’aikatan gwamnati, ma’aikatan lafiya ‘yan jarida da kuma iyaye wanda Allah ya dora musu Alhakin tabbatar da cewa sun samawa ‘ya’yansu makoma mai kyau”

Ya kuma ce tuni cutar ta bar jihar kano, bisa kokarin gwamnatin jihar na tabbatar da an inganta hanyoyin yaki da cutar, musamman ta hanyar hadaka da kungiyoyin duniya, irin sun Melinda Gate, wanda hakan yayi tasirin gaske wajen magance cutar a jihar.

Sai dai kwamishinan yace a ‘yan tsakanin an sami alamun bullar cutar a jihar Kano, wanda kuma suke zargin wasu baki ne suka shigo da ita jihar; Wanda yace kananan yara na jihar na cikin hadarin kamuwa da cutar muddin ba’a dauki matakin da ya dace ba.

“Wannan dalilin ne yasa muka ga dole mu sanar da al’umma, kuma mu yi kira garesu cewa su tabbatardukkanin yara musamman wadanda ke kasa da shekaru 5 a duniya da zarar jami’an dake allurar sun isa inda yaran suke”.

Daga bisani ya tabbatar da cewa yaran da aka samu sun kamu da wannan cuta, basu haura shekaru biyar zuwa bakwai a duniya ba, wanda hakan ke da nasaba da rashin mayar da hankali a yin allurer ta rigakafin cutar shan inna.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp