Home Labarai Shugaba Faye ya bayar da tabbacin zaɓen ‘yan majalisa bisa gaskiya da...

Shugaba Faye ya bayar da tabbacin zaɓen ‘yan majalisa bisa gaskiya da adalci

Shugaban kasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye, ya ba da tabbacin a jiya Juma’a cewa, za a gudanar da zaben ‘yan majalisar dokoki na ranar 17 ga watan Nuwamba, cikin ‘yanci da gaskiya, yana mai kira ga ‘yan siyasa da su kiyaye daga duk wani lamari da kan iya haifar da tashin hankali ko rudani.

Shugaban na Senegal ya na mai cewa “yayin da yakin neman zaben ‘yan majalisar dokoki ke gabatowa, ina gargadin dukkan ‘yan kasar Senegal, musamman ma ‘yan siyasa na ko wane bangare, da su guji wuce gona da iri a cikin maganganunsu da ayyukansu.”

Faye ya yi amfani da wannan dama tare da yin kira ga masu ruwa da tsaki da su kawo ta su goyon baya na ganin an cimma nasara a wannan zabe da sunan ceto kasar ta Senegal a karshe da kuma  tabbatar da cewa “zaben zai kasance cikin ‘yanci, dimokiradiyya da gaskiya”.

A ranar 17 ga watan Nuwamba ne ‘yan kasar Senegal za su zabi sabuwar majalisar dokoki, watanni takwas bayan zaben shugaban kasar da Diomaye Faye  ya yi nasara a zaben shugaban kasa da aka yi a zagayen farko da kashi 54% na kuri’un da aka kada. Za a fara yakin neman zaben a yau Asabar da dare.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp