Home Labarai Shugaba Faye ya bayar da tabbacin zaɓen ‘yan majalisa bisa gaskiya da...

Shugaba Faye ya bayar da tabbacin zaɓen ‘yan majalisa bisa gaskiya da adalci

Shugaban kasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye, ya ba da tabbacin a jiya Juma’a cewa, za a gudanar da zaben ‘yan majalisar dokoki na ranar 17 ga watan Nuwamba, cikin ‘yanci da gaskiya, yana mai kira ga ‘yan siyasa da su kiyaye daga duk wani lamari da kan iya haifar da tashin hankali ko rudani.

Shugaban na Senegal ya na mai cewa “yayin da yakin neman zaben ‘yan majalisar dokoki ke gabatowa, ina gargadin dukkan ‘yan kasar Senegal, musamman ma ‘yan siyasa na ko wane bangare, da su guji wuce gona da iri a cikin maganganunsu da ayyukansu.”

Faye ya yi amfani da wannan dama tare da yin kira ga masu ruwa da tsaki da su kawo ta su goyon baya na ganin an cimma nasara a wannan zabe da sunan ceto kasar ta Senegal a karshe da kuma  tabbatar da cewa “zaben zai kasance cikin ‘yanci, dimokiradiyya da gaskiya”.

A ranar 17 ga watan Nuwamba ne ‘yan kasar Senegal za su zabi sabuwar majalisar dokoki, watanni takwas bayan zaben shugaban kasar da Diomaye Faye  ya yi nasara a zaben shugaban kasa da aka yi a zagayen farko da kashi 54% na kuri’un da aka kada. Za a fara yakin neman zaben a yau Asabar da dare.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp