Home Labarai Shugaba Faye ya bayar da tabbacin zaɓen ‘yan majalisa bisa gaskiya da...

Shugaba Faye ya bayar da tabbacin zaɓen ‘yan majalisa bisa gaskiya da adalci

Shugaban kasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye, ya ba da tabbacin a jiya Juma’a cewa, za a gudanar da zaben ‘yan majalisar dokoki na ranar 17 ga watan Nuwamba, cikin ‘yanci da gaskiya, yana mai kira ga ‘yan siyasa da su kiyaye daga duk wani lamari da kan iya haifar da tashin hankali ko rudani.

Shugaban na Senegal ya na mai cewa “yayin da yakin neman zaben ‘yan majalisar dokoki ke gabatowa, ina gargadin dukkan ‘yan kasar Senegal, musamman ma ‘yan siyasa na ko wane bangare, da su guji wuce gona da iri a cikin maganganunsu da ayyukansu.”

Faye ya yi amfani da wannan dama tare da yin kira ga masu ruwa da tsaki da su kawo ta su goyon baya na ganin an cimma nasara a wannan zabe da sunan ceto kasar ta Senegal a karshe da kuma  tabbatar da cewa “zaben zai kasance cikin ‘yanci, dimokiradiyya da gaskiya”.

A ranar 17 ga watan Nuwamba ne ‘yan kasar Senegal za su zabi sabuwar majalisar dokoki, watanni takwas bayan zaben shugaban kasar da Diomaye Faye  ya yi nasara a zaben shugaban kasa da aka yi a zagayen farko da kashi 54% na kuri’un da aka kada. Za a fara yakin neman zaben a yau Asabar da dare.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp