Home General Kwankwaso ya magantu kan matsalar wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

Kwankwaso ya magantu kan matsalar wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana rashin jin daɗinsa kan rashin wutar lantar a mafi yawan jihohin Arewa.

Kamar yadda ya rubuta a shafinsa na X, Kwankwaso ya ce, “Abin takaici ne a ce mafi yawan yankunan Arewa suna zaune cikin duhun rashin wutar lantarki saboda tangarɗa a layin lantarkin 330kV wanda ya ɗauko wuta daga Shiroro zuwa Kaduna, wanda shi ne yake ba jihohin Kano da Kaduna, da layin da yake ba Bauchi da Gombe da wasu jihohin arewa maso gabas wuta.

“Matsalar ta ƙara ta’azzara ne saboda yanayin tsadar man fetur da ake ciki a Najeriya, wanda ya tilasta wa kamfanoni da kasuwanci da dama suka durƙushe.

Sannan lokacin da aka ɗauka ba a magance matsalar ba, ya nuna cewa akwai matsala a ɓangaren makamashin Najeriya,” in ji shi, inda ya ƙara da cewa akwai buƙatar a ɗauki mataki domin guje wa sake aukuwar lamarin, ta hanyar nemo wasu hanyoyin makamashin.

“Ina ba jihohin da ƴan kasuwa shawarar su zuba kuɗi a wasu hanyoyin samar da makamashin domin rage ta’allaƙa da hanyar makamashi guda ɗaya,” in ji Kwankwaso.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp