Aƙalla mutum bakwai ne suka rasu sakamakon ruhsewar wani gini a babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja.
Muƙaddashin darakta-janar na hukumar bada agajin gaggawa ta Abuja FEMA, Abdulrahman Mohammed ne ya bayyana hakan a lokacin da ya kai ziyara wajen ginin da ya rushe a kan titin hanyar tafiya filin jirgin sama.
Ya ce lamarin ya auku ne a ranar Asabar a sanadiyar wasu da suka shiga ginin, wanda hukumar kula da ingancin gine-gine ta Abuja take rusawa domin cire ƙarafa, kamar yadda Channels ta ruwaito.
Ya ce bayan waɗanda suka rasu, akwai wasu mutum da suke jinya a asibiti, sannan ya gargaɗi mutane su guji jefa rayukansu cikin hatsari ta hanyar shiga cikin gine-ginen da aka rusa.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1486 days 18 hours 59 minutes 12 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1468 days 20 hours 40 minutes 37 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com