Home Labarai Kotu ta ɗage shari’ar EFCC da Yahaya Bello zuwa Janairu

Kotu ta ɗage shari’ar EFCC da Yahaya Bello zuwa Janairu

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta ɗage sauraron ƙarar zargin almundahanar da EFCC ke yi wa tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, zuwa 21 ga watan Janairun 2025.

A zaman kotun a ranar Laraba, lauyan EFCC, Kemi Pinheiro SAN, ya ce yana da shaidu biyu da zai gabatar, sannan ya buƙaci kotun ta ci gaba da karɓar shaidu ba tare da wanda ake zargi ba ya amsa ko ya musanta zargin da ake masa ba.

Pinheiro ya ƙada da cewa, “haƙƙin amsa laifi ko musantawa ba dole ba ne, dama ce da za a iya ƙwacewa,” in ya ce wanda suke ƙara ya yi watsi da damarsa.

A nasa ɓangaren wanda ake ƙara, lauyansa, Michael Adoyi ya ce bai amince da wannan ba, inda ya ce buƙatar lauyansa masu ƙara ta ci karo da wani hukuncin kotun da ake dako.

A ƙarshe sai alƙalin kotun, mai shari’a Nwite ya ce ba zai yiwu ba a yanke hukuncin shari’ar a bana, sai ya ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa 21 ga watan Janairun 2025.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp