Home General Kace-Nace ya barke tsakanin IPMAN da Dangote

Kace-Nace ya barke tsakanin IPMAN da Dangote

Ƙungiyar dillalan man fetur ta ƙasa IPMAN, ta ce mambobinta ba sa samun loda fetur a matate man fetur ta Dangote duk da cewa sun biya naira biliyan 40 ga kamfanin NNPCL.

Shugaban IPMAN, Abubakar Garima ne bayyana haka a tashar Channels, inda ya ce sun yi mamaki da suka ji Dangote yana cewa dillalan man fetur ba sa zuwa matatarsa sayen mai.

“Idan zai sayar da mai kai-tsaye, za mu saya saboda dole sai mun biya, za a ba mu man. Yanzu haka akwai kuɗinmu naira biliyan 40 a wajen NNPCL, amma ba ma samun kayan. Kwanan nan wasu mambobinmu da NNPCL ta tura matatar Dangote, inda motocinsu suka kwashe kwana huɗu a can ba tare da sun samu man ba.”

A ranar Talata ce dai Alhaji Aliko Dangote ya gana da shugaban ƙasa Bola Tinubu, inda ya bayyana wa manema labarai bayan ganawar cewa yana litar mai sama da miliyan 500 a ajiye, amma dillalan man ba sa sayen fetur ɗin.

A ƙarshe, shugaban IPMAN, ya yi kira ga Dangote da ya duba farashin man matatarsa, sannan ya kwatanta da farashin man na ƙasashen waje. “Shin farashin ya haura na farashin da ake samu daga ƙasashen waje ko ɗaya ne? sannan wane lokaci fetur ke ɗauka kafin ya isa ga dillalin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp