Home Labarai Kotu ta ɗage shari’ar EFCC da Yahaya Bello zuwa Janairu

Kotu ta ɗage shari’ar EFCC da Yahaya Bello zuwa Janairu

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta ɗage sauraron ƙarar zargin almundahanar da EFCC ke yi wa tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, zuwa 21 ga watan Janairun 2025.

A zaman kotun a ranar Laraba, lauyan EFCC, Kemi Pinheiro SAN, ya ce yana da shaidu biyu da zai gabatar, sannan ya buƙaci kotun ta ci gaba da karɓar shaidu ba tare da wanda ake zargi ba ya amsa ko ya musanta zargin da ake masa ba.

Pinheiro ya ƙada da cewa, “haƙƙin amsa laifi ko musantawa ba dole ba ne, dama ce da za a iya ƙwacewa,” in ya ce wanda suke ƙara ya yi watsi da damarsa.

A nasa ɓangaren wanda ake ƙara, lauyansa, Michael Adoyi ya ce bai amince da wannan ba, inda ya ce buƙatar lauyansa masu ƙara ta ci karo da wani hukuncin kotun da ake dako.

A ƙarshe sai alƙalin kotun, mai shari’a Nwite ya ce ba zai yiwu ba a yanke hukuncin shari’ar a bana, sai ya ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa 21 ga watan Janairun 2025.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp