Home General Wutar Lantarki zata dawo Arewa nan da sati 2

Wutar Lantarki zata dawo Arewa nan da sati 2

Gwamantin tarayya Najeriya ta ce tana iya bakin kokarinta wajen dawo da wutar lantarkin yankin arewacin kasar da ta kwashe tsahon mako guda yana cikin duhu.

Ministan Makamashi, Adebayo Adelabu ne  ya bayyana hakan, in da yace wutar yakin zata dawo aiki nan da kwanaki 14 masu zuwa.

yakin na arewaci na dauke da jihohi 17 wanda suka kasance cikin duhun rashin wutar tun ranar talata 12 ga watan Nuwamba, 2024.

Adelabu, yayi da yake amsa tambaya daga bakin wani sanata a majalisar tarayyar kasar, yace wani yanki na aikin zai kammala nan da kwanaki 3 masu zuwa.

A dai tsakanin nan ne Kungiyar tuntubar juna ta dattawan arewacin Najeriya, ACF ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ayyana dokar ta-ɓaci kan ɓangaren wutar lantarki a daidai lokacin da yankin arewacin ƙasar ke ci gaba da kasancewa cikin duhu sakamakon rashin wuta.

Ƙungiyar gwamnomin arewacin Najeriyar ita ma ta yi kira ga gwamnatin Tarayya da ta gaggauta kawo ƙarshen matsalar.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp