Home General NNPLC ya sake kara farashin Man Fetur a Najeriya

NNPLC ya sake kara farashin Man Fetur a Najeriya

NNPCL

A karo na biyu kamfanin man Fetur na Nijeriya ya sake kara kudin Man abin da ya haifar da kace nace da mamaki bayan karin da yazo a ba zata ranar Talata 29 ga Oktoba 2024, wanda wannan shine Karo na biyu da kamfanin yayi ƙari cikin makonni uku.

Kamfanin man na kasa ya kara farashin daga naira 1,030 zuwa 1060 a Babban Birnin Tarayya Abuja, yayin da a Jihar Legas farashin ya koma Naira 1,025 daga 998 a kowacce lita.

Kafin wannan ƙarin, ana sayar da litar man fetur ne a  kan N897 a Abuja, a Legas kuma N885, amma a ranar 9 ga watan Oktoba da muke bankwana da shi aka ƙara na Legas zuwa N998, na Abuja kuma zuwa N1,030.

Ķarin kudin na zuwa ne duk da fara aikin Matatar Man Ɗangote, wadda ake tunanin za ta kawo sauki da wadatuwar man a ƙasar.

Tun bayan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanar da janye Tallafin mai a watan mayun 2023, NNPCL ya ƙara kudin fetir daga 184 zuwa 1,025 a Jihar Legas.

Masana dai na ganin wannan wani mataki ne da zai kara jefa yan Najeriya cikin mawuyacin hali, dama tuni wasu suka ajiye ababen hawan su saboda tsadar farashin man.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp