Home Labarai Mutum 10 sun mutu, yayin da bakwai suka jikkata bayan rushewar gini...

Mutum 10 sun mutu, yayin da bakwai suka jikkata bayan rushewar gini a Ibadan

Aƙalla mutum 10 ne suka mutu yayainwa su bakwai suka jikkata bayan faɗuwar gini a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

Cikin wata sanarwa da hukumar kashe gobara ta jihar ta fitar, ta ce lamarin ya faru da tsakar daren da ya gabata a unguwar Jegeda Oluloyo da ke binrin na Ibadan, kamar yadda Jaridar unch ya ruwaito.

Sanarwar ta ƙara da cewa yayin da aka zaƙulo gawarwarkin mutum 10 daga cikin ɓaraguzan ginin, an kuma ceto wasu mutum bakwai da raunuka, sannan an ci gaba da aikin ceton domin nemo ƙarin mutane.

Faɗuwar gine-gine dai wani lamari ne da ke neman zaman ruwan dare a Najeriya, inda da dama takan zo da asarar rayuka masu yawa.

Mahukuntar ƙasar na ɗora alhakin matsalar kan rashin bin ingantaccen tsari da ƙa’ida a lokacin yin gine-ginen.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp