Home DUNIYA EU da Jamus sun bai wa Najeriya tallafin kusan yuro miliyan 18

EU da Jamus sun bai wa Najeriya tallafin kusan yuro miliyan 18

Kungiyar tarayyar turai da ƙasar Jamus sun ƙaddamar da kaso na 3 na shirin tallafawa Najeriya dangane da abinda ya shafi makamashi NESP domin habbaka sabbin hanyoyin samar da isashshen makamashi musamman a yankunan karkara.

Shirin zai laƙume kuɗin da ya kusa yuro miliyan 18 inda za a sada mutane 1,500 da lantarki da kuma samarwa da mutane dubu 30 gas na girki.

Har wa yau a kashi na 3 na wannan shirin za a samar da wutar lantarki mai ƙarfin Megawatts 8.

Tallafin na samar da makamashi ga Najeriya an fara ƙaddamar da shi tun a shekarar 2013 wanda kungiyar tarayyar turai EU da tallafin ƙasar Jamus haɗin gwiwa da ma’aikatar lantarki ta Najeiya.

Kungiyar ta tarayyar turai ta amince ta ƙara zuba kuɗi a kashi na 3 na wannan shiri domin taimakawa ci gaban da kuma samar da tsarin lantarki ta sabbin hanyoyin makamashi da kuma tabbatar da jama’a sun amafana da shirin.

Mataimakin Ambasadan ƙasar Jamus Johannes Lenhre ya tabbatar da shiri ƙasarsa wurin cimma muradan da Najeriya ta snaya a gaba a fannin makamashi.

Sakataran ma’aikatar lantarki a Najeriya Mahmuda Mamman ya yaba da irin tallafin da Najeriya ke samu daga kungiyar tarayyar turai da Jamus musamman yadda suke ƙoƙarin tabbatar da samun isashshen makamashi a ƙasar

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp