Home General Gwamna Kano ya Magantu kan yaran da aka kai Kotu bisa zargin...

Gwamna Kano ya Magantu kan yaran da aka kai Kotu bisa zargin shiga zanga-zanga

Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sha alwashin yin duk mai yiwuwa don ganin ya dawo da yaran kano da aka kai su Kotu a Abuja bisa zarginsu da shiga zanga-zangar tsadar rayuwa.

Idan za a iya tunawa an gudanar da Zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a duk fadin Nijeriya a ranar 1 ga watan Agusta da ya gabata.

Yayin zanga-zanga yan sanda sun kama Matasa da dama musamman wadanda suka rika daga tutar kasar Rasha, wanda hakan tasa a ranar juma’ar nan aka gurfanar da su a gaban wata kotu dake Abuja.

Yanayin da aka nuna yaran lokacin da suka shiga cikin kotun ya tayar da hankulan al’umma musamman yan Arewacin Nigeria, saboda ana ganin mafi yawan yaran an Kamo su ne daga jihohin Arewacin Nigeria musamman Kano.

Hakan tasa al’umma suke ta kiraye-kiraye musamman ga shugabanni Arewacin Nigeria da su sanya baki a sako yaran kasancewarsu kananan yara kuma duk an barsu cikin yunwa da kaskananci.

A daren jiya juma’a gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nuna rashin jin dadinsa da halin da yaran suke cikin.

A wani rubutu da ya gwamnan ya wallafa a sashin shafinsa na Facebook ya an jawo hankalin Kan batun yaran, Inda yace tuni ya umarci babban lauyan jihar kano kuma kwamishinan Shari’ar da yayi duk abun da ya kamata domin karɓo yaran da suke yan Kano a cikin su.

Al’ummar dai yana ta kiraye-kirayen ya kamata shugabannin arewa su dauki matakan da suka dace domin ganin ba a cigaba da rike yarana ana azabtar da su ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp