Home General Wasan kwaikwayo ne faduwar da yara 6 da aka kai kotu suka...

Wasan kwaikwayo ne faduwar da yara 6 da aka kai kotu suka yi – IG

Faduwar da yaran da ake zargi da shiga zanga-zanga su ka yi a kotu shiri ne – Babban Sifeton Ƴansanda

Sufeto-Janar na ‘Yansanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana cewa yanke jiki da faduwa da wasu yara shida da ake zargi da zanga-zanga suka yi a kotu kafin gabatar da su a gaban alkali ya kasance wani shiri ne da aka tsara don jan hankalin jama’a ga abin da ba daidai ba.

Egbetokun ya jaddada cewa, duk da haka, an ba da taimakon likita cikin gaggawa, ya na mai bayyana cewa ‘yansanda su na da alhakin kula da lafiyar wadanda suke tsare.

A ranar Juma’a, an gurfanar da mutane 76, yawancinsu kananan yara wadanda ke fama da rashin isasshen abinci, a gaban kotu dangane da zanga-zangar #EndBadGovernance. Goma sha shida daga cikinsu sun fadi kuma aka fitar dasu daga cikin kotun.

Bayan gurfanar da su, kotu ta ba kowanne yaro beli wanda aka sa a kan Naira miliyan goma. Wannan al’amari ya haifar da suka a gida da waje.

Jaridar PUNCH ta rawaito cewa a wata sanarwa mai kwanan wata Nuwamba 1, da mai magana da yawun rundunar Muyiwa Adejobi ya sanya wa hannu a madadin Sufeto-Janar din, Egbetokun ya tabbatar da cewa, a karkashin dokar Najeriya, wadanda suka kai shekarun aikata laifuka sun isa a hukunta su duk da karancin shekarunsu.

Ya ce, “A yau, wani abu da ba a zata ba ya faru a kotu inda wasu shida daga cikin wadanda ake zargi suka yi gaggawar fita daga kotu kuma suka yanke jiki suka fadi , suna jan hankalin kafofin watsa labarai a wani yunkuri da aka shirya don jan hankali ga abin da ba daidai ba.”

“A kwanan nan rundunar ƴansanda ta ƙasa ta gurfanar da mutane 76 da ake zargi da aikata ta’addanci, cin amanar kasa da kone-kone. Wadannan Laifuka ne manya da su ka sa ake tsare da wadanda ake zargi.

“Tun lokacin da aka fara shari’ar nan, rundunar ƴansanda ta dage wajen bin ƙa’idojin Shari’a domin yi wa waɗanda ake zargin adalci,” in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp