Home General Gwamna Kano ya Magantu kan yaran da aka kai Kotu bisa zargin...

Gwamna Kano ya Magantu kan yaran da aka kai Kotu bisa zargin shiga zanga-zanga

Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sha alwashin yin duk mai yiwuwa don ganin ya dawo da yaran kano da aka kai su Kotu a Abuja bisa zarginsu da shiga zanga-zangar tsadar rayuwa.

Idan za a iya tunawa an gudanar da Zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a duk fadin Nijeriya a ranar 1 ga watan Agusta da ya gabata.

Yayin zanga-zanga yan sanda sun kama Matasa da dama musamman wadanda suka rika daga tutar kasar Rasha, wanda hakan tasa a ranar juma’ar nan aka gurfanar da su a gaban wata kotu dake Abuja.

Yanayin da aka nuna yaran lokacin da suka shiga cikin kotun ya tayar da hankulan al’umma musamman yan Arewacin Nigeria, saboda ana ganin mafi yawan yaran an Kamo su ne daga jihohin Arewacin Nigeria musamman Kano.

Hakan tasa al’umma suke ta kiraye-kiraye musamman ga shugabanni Arewacin Nigeria da su sanya baki a sako yaran kasancewarsu kananan yara kuma duk an barsu cikin yunwa da kaskananci.

A daren jiya juma’a gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nuna rashin jin dadinsa da halin da yaran suke cikin.

A wani rubutu da ya gwamnan ya wallafa a sashin shafinsa na Facebook ya an jawo hankalin Kan batun yaran, Inda yace tuni ya umarci babban lauyan jihar kano kuma kwamishinan Shari’ar da yayi duk abun da ya kamata domin karɓo yaran da suke yan Kano a cikin su.

Al’ummar dai yana ta kiraye-kirayen ya kamata shugabannin arewa su dauki matakan da suka dace domin ganin ba a cigaba da rike yarana ana azabtar da su ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp