Home General Gwamna Kano ya Magantu kan yaran da aka kai Kotu bisa zargin...

Gwamna Kano ya Magantu kan yaran da aka kai Kotu bisa zargin shiga zanga-zanga

Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sha alwashin yin duk mai yiwuwa don ganin ya dawo da yaran kano da aka kai su Kotu a Abuja bisa zarginsu da shiga zanga-zangar tsadar rayuwa.

Idan za a iya tunawa an gudanar da Zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a duk fadin Nijeriya a ranar 1 ga watan Agusta da ya gabata.

Yayin zanga-zanga yan sanda sun kama Matasa da dama musamman wadanda suka rika daga tutar kasar Rasha, wanda hakan tasa a ranar juma’ar nan aka gurfanar da su a gaban wata kotu dake Abuja.

Yanayin da aka nuna yaran lokacin da suka shiga cikin kotun ya tayar da hankulan al’umma musamman yan Arewacin Nigeria, saboda ana ganin mafi yawan yaran an Kamo su ne daga jihohin Arewacin Nigeria musamman Kano.

Hakan tasa al’umma suke ta kiraye-kiraye musamman ga shugabanni Arewacin Nigeria da su sanya baki a sako yaran kasancewarsu kananan yara kuma duk an barsu cikin yunwa da kaskananci.

A daren jiya juma’a gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nuna rashin jin dadinsa da halin da yaran suke cikin.

A wani rubutu da ya gwamnan ya wallafa a sashin shafinsa na Facebook ya an jawo hankalin Kan batun yaran, Inda yace tuni ya umarci babban lauyan jihar kano kuma kwamishinan Shari’ar da yayi duk abun da ya kamata domin karɓo yaran da suke yan Kano a cikin su.

Al’ummar dai yana ta kiraye-kirayen ya kamata shugabannin arewa su dauki matakan da suka dace domin ganin ba a cigaba da rike yarana ana azabtar da su ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp