Home General Gwamna Kano ya Magantu kan yaran da aka kai Kotu bisa zargin...

Gwamna Kano ya Magantu kan yaran da aka kai Kotu bisa zargin shiga zanga-zanga

Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sha alwashin yin duk mai yiwuwa don ganin ya dawo da yaran kano da aka kai su Kotu a Abuja bisa zarginsu da shiga zanga-zangar tsadar rayuwa.

Idan za a iya tunawa an gudanar da Zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a duk fadin Nijeriya a ranar 1 ga watan Agusta da ya gabata.

Yayin zanga-zanga yan sanda sun kama Matasa da dama musamman wadanda suka rika daga tutar kasar Rasha, wanda hakan tasa a ranar juma’ar nan aka gurfanar da su a gaban wata kotu dake Abuja.

Yanayin da aka nuna yaran lokacin da suka shiga cikin kotun ya tayar da hankulan al’umma musamman yan Arewacin Nigeria, saboda ana ganin mafi yawan yaran an Kamo su ne daga jihohin Arewacin Nigeria musamman Kano.

Hakan tasa al’umma suke ta kiraye-kiraye musamman ga shugabanni Arewacin Nigeria da su sanya baki a sako yaran kasancewarsu kananan yara kuma duk an barsu cikin yunwa da kaskananci.

A daren jiya juma’a gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nuna rashin jin dadinsa da halin da yaran suke cikin.

A wani rubutu da ya gwamnan ya wallafa a sashin shafinsa na Facebook ya an jawo hankalin Kan batun yaran, Inda yace tuni ya umarci babban lauyan jihar kano kuma kwamishinan Shari’ar da yayi duk abun da ya kamata domin karɓo yaran da suke yan Kano a cikin su.

Al’ummar dai yana ta kiraye-kirayen ya kamata shugabannin arewa su dauki matakan da suka dace domin ganin ba a cigaba da rike yarana ana azabtar da su ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp