Home General IPMAN ta cimma matsaya da Dangote kan sayen fetur

IPMAN ta cimma matsaya da Dangote kan sayen fetur

Ƙungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Najeriya IPMAN ta ce mambobinta sun cimma matsaya domin fara sayen man fetur daga matatar man Dangote kai-tsaye.

Shugaban ƙungiyar ta IPMAN na ƙasa, Abubakar Garima, shi ya bayyana haka a Abuja ranar Litinin bayan uwar ƙungiyar ta gudanar da taro da mambobinta.

Ya ce haɗin gwiwa da Dangote zai saka a samu wadataccen man fetur cikin sauki a faɗin ƙasar.

“Ina farin cikin sanar da cewa matatar Dangote ta amince ta fara sayar mana da man fetur da kuma dizel kai-tsaye domin rarrabawa a defo-defo ɗin mu da kuma sauran gidajen mai,” in ji Girima.

Ya buƙaci mambobin IPMAN ɗin da su mara wa matatar Dangote baya, inda ya ce hakan zai kuma farfaɗo da yanayin hada-hadar man fetur da kuma rage ƙarancinsa da ake samu a ƙasar.

Abubakar ya ce matakin zai kuma janyo bunƙasar ɓangaren man fetur ɗin Najeriya.

Matatar ta Dangote ta yi alkawarin fara sayar da man fetur ɗin ga mambobin IPMAN sama da 30,000 da kuma gidajen mai 150,000 a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp