Home General Atiku yayi martani ga fadar shugaban kasa kan batun hassada

Atiku yayi martani ga fadar shugaban kasa kan batun hassada

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya ce ba ya yi wa Tinubu hassada, inda ya ce ya jefa ƴan Najeriya cikin kunci.

Ɗan takarar shugaban ƙasar karkashin jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, na mayar da martani kan kalamai da fadar shugaban Najeriyar ta yi cewa yana ƙyashi tare da baƙin ciki da matsayin Shugaba Bola Tinubu na shugaban ƙasa.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya fitar ranar Lahadi, ya soki Atiku kan ci gaba da sukar tsare-tsaren tattalin arzikin da shugaban, maimakon mayar da hankali kan matsalolin jam’iyyarsa.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar dai ya sha sukar tsare-tsare da gwamnatin Tinubu ta ɓullo da su, musamman na tattalin arziki, inda ya ce babu abin da za su haifar illa jefa ƴan Najeriya cikin kunci da wahala.

Wata sanarwa da mai taimakawa Atiku na musamman kan yaɗa labarai Phrank Shaibu ya fitar ranar Litinin, Atiku ya ce sai Tinubu ya aiwatar da tsare-tsare kafin yake duba illolin da za su haifar.

“Tinubu bai shiryawa mulki ba. Sai ya aiwatar da abu kafin yake duba illarsa daga baya. Wannan shi ya sa ya sanar da janye tallafin man fetur ba tare da kawo abin da zai rage wa ƴan ƙasar raɗaɗi ba.

“Abin mamaki ne a yi iƙirarin cewa Atiku na kyashin Tinubu. Ba zai yi hassada da Tinubu ba saboda irin kunci da ya jefa ƴan Najeriya,” in ji sanarwar.

Atiku ya ce babu wani adalin shugaba wanda yake da zimmar ganin ƴan Najeriya cikin walwala da zai yi hassada da irin gallazawa da ake yi musu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp