Home General IPMAN ta cimma matsaya da Dangote kan sayen fetur

IPMAN ta cimma matsaya da Dangote kan sayen fetur

Ƙungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Najeriya IPMAN ta ce mambobinta sun cimma matsaya domin fara sayen man fetur daga matatar man Dangote kai-tsaye.

Shugaban ƙungiyar ta IPMAN na ƙasa, Abubakar Garima, shi ya bayyana haka a Abuja ranar Litinin bayan uwar ƙungiyar ta gudanar da taro da mambobinta.

Ya ce haɗin gwiwa da Dangote zai saka a samu wadataccen man fetur cikin sauki a faɗin ƙasar.

“Ina farin cikin sanar da cewa matatar Dangote ta amince ta fara sayar mana da man fetur da kuma dizel kai-tsaye domin rarrabawa a defo-defo ɗin mu da kuma sauran gidajen mai,” in ji Girima.

Ya buƙaci mambobin IPMAN ɗin da su mara wa matatar Dangote baya, inda ya ce hakan zai kuma farfaɗo da yanayin hada-hadar man fetur da kuma rage ƙarancinsa da ake samu a ƙasar.

Abubakar ya ce matakin zai kuma janyo bunƙasar ɓangaren man fetur ɗin Najeriya.

Matatar ta Dangote ta yi alkawarin fara sayar da man fetur ɗin ga mambobin IPMAN sama da 30,000 da kuma gidajen mai 150,000 a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp