Home General Wutar lantarki a Arewacin Najeriya ta sake lalacewa – TCN

Wutar lantarki a Arewacin Najeriya ta sake lalacewa – TCN

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Ƙasa, TCN, ya bayyana cewa bata-gari sun lalata layin wuta mai karfin 33KV daga Lokoja zuwa Gwagwalada.

Wannan na kunshe ta cikin wa sanarwa da Manajan yaɗa labarai na kamfanin, Ndidi Mbah, ta fitar a ranar Lahadi, wadda tace ɓatagarin sun lalata rumbun raba wutar lantarki na T306, T307 da kuma T308 a ranar Asabar.

Ta ce sun kuma sace wayoyin alminiyon har dauri biyu.

A cewar Ndidi, an gano hakan ne bayan da TCN ya tashi ma’aikatan sa don gano musabbabin katsewar wutar lantarki da safiyar Asabar.

Sai dai ta ce an fara kokarin gyaran matsalar, inda ta baiwa al’ummar yankin da ma sauran da ke kan layin wutar hakuri.

Matsalar wutar lantarki ta sha na daga cikin matsaloli na baya bayannan dake jifa al’ummar yankin cikin mawuyacin hali da asarar dukiya mai tarin yawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp