Home General Wutar lantarki a Arewacin Najeriya ta sake lalacewa – TCN

Wutar lantarki a Arewacin Najeriya ta sake lalacewa – TCN

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Ƙasa, TCN, ya bayyana cewa bata-gari sun lalata layin wuta mai karfin 33KV daga Lokoja zuwa Gwagwalada.

Wannan na kunshe ta cikin wa sanarwa da Manajan yaɗa labarai na kamfanin, Ndidi Mbah, ta fitar a ranar Lahadi, wadda tace ɓatagarin sun lalata rumbun raba wutar lantarki na T306, T307 da kuma T308 a ranar Asabar.

Ta ce sun kuma sace wayoyin alminiyon har dauri biyu.

A cewar Ndidi, an gano hakan ne bayan da TCN ya tashi ma’aikatan sa don gano musabbabin katsewar wutar lantarki da safiyar Asabar.

Sai dai ta ce an fara kokarin gyaran matsalar, inda ta baiwa al’ummar yankin da ma sauran da ke kan layin wutar hakuri.

Matsalar wutar lantarki ta sha na daga cikin matsaloli na baya bayannan dake jifa al’ummar yankin cikin mawuyacin hali da asarar dukiya mai tarin yawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp