Home General Inganta Lafiya ne Babbar Manufata – Mahmud Tajo Gaya

Inganta Lafiya ne Babbar Manufata – Mahmud Tajo Gaya

An Bawa al’ummar ƙaramar hukumar Gaya tabbacin inganta harkar lafiya a yankin yadda ya kamata saboda muhimmancinta ga rayuwar al’umma.

Sabon zaɓaɓɓen shugaban ƙaramar hukumar, Mahmud Tajo Gaya ne ya bayyana haka yayin wata ganawa ta musamman da Sashin Hulɗa da Jama’a na Ma’aikatar Lafiya lokacin da tawagar duba aikin rigakafin shan-inna da aka kammala kwanan nan ta ziyarci yankin, inda aka yi tattaunawar a ofishin Shirin Rigakafi na Ƙasa (NPI) reshen yankin.

Tajo Gaya ya ce yana da sha’awa game da lafiya kasancewar tun asali shi ma’aikacin lafiya ne, kuma tsohon Babban mai Taimaka wa Gwamna na Musamman a kan Asibitin Tafi da Gidanka, da ake duba mutane a faɗin jihar Kano da ba su magani kyauta musamman a wurare masu nisa da wahalar shiga.

Ya ce ya tsotsi sha’awar inganta lafiya ne daga wajen Gwamnan lafiya, Alhaji Abba Kabir Yusuf, da Kwamishinan Lafiya Dakta Abubakar Labaran Yusuf, da hakan ya tsima shi bayan an zaɓe shi ya ƙudiri aniyar inganta fannin lafiya na ƙaramar hukumar Gaya ta hanyar bijiro da hanyoyi daban-daban domin sauƙaƙa wa al’ummarsa.

“Tun da na shiga ofis ban huta ba. Na ziyarci cibiyoyin lafiya na yankin don ganin yadda abubuwa ke tafiya. Nan da nan na ba da umarnin ɗaga likkafar asibitoci biyar su rinƙa yin aiki cikin awanni 24. Zan ci gaba da tallafa wa duk wani shiri da zai taimaki al’ummarmu. Babban abin da na sa a gaba shi ne, inganta lafiya, lafiya, lafiya.

“Lokacin na na zo na tarar akwai cutar kwalara nan da can a wasu sassa na ƙaramar hukumar da ta shafi kimanin mutane hamsin kwance a asibitoci. Mun kula da su har aka sallame su, sannan na bai wa kowane daga cikinsu Naira 10,000,” ya bayyana.

Shugaban ƙaramar hukumar ya ce yana da shirin inganta ƙwarewa da ilimin ma’aikatan lafiya domin a ƙara musu karsashi ta yadda za su yi abin da ya kamata, ya ƙara da cewa abin da yake so daga gare su shi ne su zama masu gaskiya da riƙon amana yayin gudanar da aikinsu domin a inganta tsarin lafiya a ƙaramar hukumar.

Ya nuna gamsuwa da yadda ya samu sashin da sadaukarwar da ma’aikatan lafiya ke nunawa yayin da suke gudanar da ayyukansu a cibiyoyin lafiya daban-daban, ya hore su da su riɓanya kokari domin al’ummar ƙaramar hukumar su amfana sosai.

Tajo Gaya ya ce ya zauna da ma’aikatan sashin lafiyar inda ya yabe su a inda suka yi bajinta tare da yi musu gyara a inda yake ganin akwai buƙatar haka, kuma suka amince, yana mai nuna farin ciki da gudunmawar da ƙungiyoyi masu tallafa wa lafiya ke bayarwa a yankin.

Ya gode wa al’ummar ƙaramar hukumar bisa goyon bayan da suke ba shi tun lokacin da ya zo tare da yin kira gare su da su ci gaba da mara wa manufofi da tsare-tsaren da ya zo da su na ciyar da karamar hukumar gaba baya, yana mai tabbatar musu da shimfiɗa ingantaccen shugabanci.

Sa Hannu:
Ibrahim Abdullahi
Jami’in Yaɗa Labarai
Ma’aikatar Lafiya
9 ga Nuwamba 2024

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp