Home General Babban Sufeton Ƴansanda ya hana Amotekum aiki a zaɓen gwamnan Ondo

Babban Sufeton Ƴansanda ya hana Amotekum aiki a zaɓen gwamnan Ondo

Babban Sufeton ƴansandan Najeriya Kayode Egbetokun ya haramta wa ƙungiyar tsaro ta jihohin kudu maso yamma da ake wa lakabi da Amotekun da ‘yansintiri na Vigilante da sauran ire-irensu shiga harkokin zaɓen gwamnan jihar Ondo.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan na ƙasa Auyiwa Adejobi ya fitar a yau Lahadi, ya ce Babban Sufeton ya bayar da umarnin tura jami’an ‘yansanda daga ɓangarori daban-daban na rundunar domin aikin zaɓen.

Aƙalla jam’iyyu 17 ne aka bayar da rahoton cewa za su shiga zaɓen wanda za a yi ranar Asabar mai zuwa, 16 ga watan Nuwamba, 2024.

Sanarwar ta ce ‘yansanda da sauran hukumomin tsaro na tarayya ne za su aikin tabbatar da tsaro a lokacin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp