Home General Babban Sufeton Ƴansanda ya hana Amotekum aiki a zaɓen gwamnan Ondo

Babban Sufeton Ƴansanda ya hana Amotekum aiki a zaɓen gwamnan Ondo

Babban Sufeton ƴansandan Najeriya Kayode Egbetokun ya haramta wa ƙungiyar tsaro ta jihohin kudu maso yamma da ake wa lakabi da Amotekun da ‘yansintiri na Vigilante da sauran ire-irensu shiga harkokin zaɓen gwamnan jihar Ondo.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan na ƙasa Auyiwa Adejobi ya fitar a yau Lahadi, ya ce Babban Sufeton ya bayar da umarnin tura jami’an ‘yansanda daga ɓangarori daban-daban na rundunar domin aikin zaɓen.

Aƙalla jam’iyyu 17 ne aka bayar da rahoton cewa za su shiga zaɓen wanda za a yi ranar Asabar mai zuwa, 16 ga watan Nuwamba, 2024.

Sanarwar ta ce ‘yansanda da sauran hukumomin tsaro na tarayya ne za su aikin tabbatar da tsaro a lokacin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp