Majalisar wakilai ta amince Tinubu ya ciwo bashi

Majalisar dattawa ta amince da bukatar shugaban kasa Bola Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.2.

Majalisar dattijai ta amince da bukatar ciyo bashin ne bayan da ta yi nazari kan rahoton Aliyu Wamakko, shugaban kwamitin kula da basussukan cikin gida da na kasashen waje.

Kudaden da Tinubu zai ciyo bashin a kudin Naira ya kai kwatankwacin Naira Tiriliyan 1.7 , za dai a yi amfani da Kudaden ne domin cike gibin Naira Tiriliyan 9.1 a kasafin kudin 2024.

A ranar talata ne dai Shugaba Tinubu ya bukaci majalisar dattawan da ta amince masa ya ciyo wannan bashin.

Majalisar zartaswa ta Nigeriya (FEC) ce ta fara amincewa a da shirin karɓo bashin na dala biliyan 2.2 don “karfafa kudaden kasar da kuma bunkasa tattalin arzikin kasar”.

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1465 days 10 hours 46 minutes 38 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1447 days 12 hours 28 minutes 3 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com