Home General Yanzu-yanzu: Majalisar Wakilai ta ki amincewa da kudirin neman karawa shugaban kasa...

Yanzu-yanzu: Majalisar Wakilai ta ki amincewa da kudirin neman karawa shugaban kasa wa’adi

Majalisar wakilai ta yi watsi da kudirin dokar da ke neman mayar da wa’adin shugabancin Najeriya ya koma shekaru shida, amma falle daya.

An yi watsi da kudirin dokar, wanda ake shirin yiwa karatu na biyu a yayin zaman taron na ranar Alhamis.

Kudirin dokar dai da ya wuce zai sauya tanade-tanaden kundin tsarin mulkin Nigeriya, na samar da wa’adin mulki na shekaru shida ga shugaban kasa da gwamnonin jihohi.

Hon. Ikenga Ugochinyere ne ya gabatar da kudirin , Wanda ya bukaci wa’adin mulkin Shugaban kasa da gwamnoni da shugabannin kananan hukumomi ya koma falle daya amma ya kai shekaru shida .

Kudirin ya kuma nemi a ba da damar gudanar da dukkan zabukan shugaban kasa, gwamna da yan majalisu duk a rana daya.

A lokacin da aka kada kuri’a a kan kudirin dokar da aka shirya yi wa karatu na biyu, yawancin ‘yan majalisar sun kada kuri’ar kin amincewa da shi.

Idan za a iya tunawa a kwanakin baya tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya bayar da shawarar a gyara kundin tsarin mulkin kasar na 1999 da dokar zabe ta 2022, saboda a bada dama wa’adin shugaban kasa ya koma na tsawon shekaru shida, sannan a rika baiwa kowacce shiyya dama.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp