Home General Sojojin Nijeriya sun kwato litar mai dubu 80 a yankin Niger Delta

Sojojin Nijeriya sun kwato litar mai dubu 80 a yankin Niger Delta

Sojojin Nijeriya sun sami nasarar kwato litar man fetur dubu 80 da aka sace a yankin Niger Delta.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mukaddashin mataimakin daraktan yada labaran rundunar sojin ta 6 Laftanar kanal Danjuma Jonah Danjuma ya fitar a ranar lahadi, wadda ta ce dakarun sojojin shiyya ta 6 sun gudnar da wani sumame a daga rabar 18 zuwa 24 ga watan Nuwamban 2024.

a wani bangare na kakkabe masu yin zagon kasa ga tattalin arzikin yankin na Niger delta dake da arzikin man fetur.

sanarwar ta ce a jihar Bayelsa dakarun sun gudanar da sumame masu tarin yawa wanda ya suka sami nasarori, inda a karamar hukumar Ekeremor suka kama wani jingin ruwan katako dake dauke da lita sama da dubu 2 da dari 5 da aka sato.

haka kuma a garin Sangakubu da ke karamar hukumar Nembe, dakarun sun sami nasarar bankado matatar mai da bata garin ke aiki da ita ba bisa kaida ba, dakarun sun fadada ayyukan zuwa karamar kudancin Ijaw a yankin Tebidaba Creek, in da suka kame wani jirgin ruwan dauke wasu ma’adanai da aka sata.

yayin sumamen, dakarun sojojin sun lalata matatun mai 34 da ake gudanar da su ba bisa ka’idaba, gami da kama mutane 11 da ake zargi da satar mai da kananan jiragen ruwa 19.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp