Home General Ƙungiyar dattawan arewa ta yi watsi da Ƙudurin dokar sake fasalin haraji

Ƙungiyar dattawan arewa ta yi watsi da Ƙudurin dokar sake fasalin haraji

Kungiyar Dattawan Arewa ta NEF ta yi watsi da kudurin dokar sake fasalin haraji, tare da gargadin cewa yana barazana ga hadin kan kasa. Kungiyar ta soki yadda aka aiwatar da ita, inda ta yi zargin cewa an mayar da masu ruwa da tsaki ciki har da mambobin majalisar tattalin arzikin kasa a gefe yayin gudanar da aikin.

Shugaban kungiyar Dattawan Arewa, Farfesa Ango Abdullahi, bayan taron kwamitin amintattu na karo na biyu na shekara-shekara, a Abuja ya bayyana haka.

Kungiyar ta yabawa kungiyar gwamnonin jihohin Arewa da kuma majalisar sarakunan arewacin Najeriya da suka nuna adawa da kudurin, inda suka bayyana matsayarsu a matsayin ‘yan kishin kasa, tare da yin kira ga ‘yan siyasar Arewa a majalisar dokokin kasar da su tofa albarkacin bakinsu.

Taron ya yi nuni da cewa, a halin da ake ciki yanzu, dokar sake fasalin haraji an yi shi ne da nufin tursasawa yan kasar, kuma hakan barazana ce ga hadin kanmu da hadin kan kasa.

“Taron ya ci gaba da jawo hankulan mutane kan hanyar da ba ta dace ba da kuma yadda aka sanya dokar sake fasalin haraji a kan al’umma, ba tare da ba da damar shigar da masu ruwa da tsaki ba, kamar yadda ya sanya mambobin majalisar tattalin arzikin kasa cikin duhu.

“Majalisar, ta yi Allah-wadai da kakkausar murya, da irin hasarar murya da aka yi a kan wannan batu na yawan zababbun ’yan siyasa da suka fito daga yankin, tare da yi musu gargadi da kakkausar murya.

Kungiyar ta NEF ta bukaci ‘yan Arewa da su kara taka tsan-tsan wajen kare hakkinsu, musamman a lokacin zabe, ta kuma yi gargadin cewa kada su fada cikin magudin shugabanni marasa kishin kasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp