Home General Ƙungiyar dattawan arewa ta yi watsi da Ƙudurin dokar sake fasalin haraji

Ƙungiyar dattawan arewa ta yi watsi da Ƙudurin dokar sake fasalin haraji

Kungiyar Dattawan Arewa ta NEF ta yi watsi da kudurin dokar sake fasalin haraji, tare da gargadin cewa yana barazana ga hadin kan kasa. Kungiyar ta soki yadda aka aiwatar da ita, inda ta yi zargin cewa an mayar da masu ruwa da tsaki ciki har da mambobin majalisar tattalin arzikin kasa a gefe yayin gudanar da aikin.

Shugaban kungiyar Dattawan Arewa, Farfesa Ango Abdullahi, bayan taron kwamitin amintattu na karo na biyu na shekara-shekara, a Abuja ya bayyana haka.

Kungiyar ta yabawa kungiyar gwamnonin jihohin Arewa da kuma majalisar sarakunan arewacin Najeriya da suka nuna adawa da kudurin, inda suka bayyana matsayarsu a matsayin ‘yan kishin kasa, tare da yin kira ga ‘yan siyasar Arewa a majalisar dokokin kasar da su tofa albarkacin bakinsu.

Taron ya yi nuni da cewa, a halin da ake ciki yanzu, dokar sake fasalin haraji an yi shi ne da nufin tursasawa yan kasar, kuma hakan barazana ce ga hadin kanmu da hadin kan kasa.

“Taron ya ci gaba da jawo hankulan mutane kan hanyar da ba ta dace ba da kuma yadda aka sanya dokar sake fasalin haraji a kan al’umma, ba tare da ba da damar shigar da masu ruwa da tsaki ba, kamar yadda ya sanya mambobin majalisar tattalin arzikin kasa cikin duhu.

“Majalisar, ta yi Allah-wadai da kakkausar murya, da irin hasarar murya da aka yi a kan wannan batu na yawan zababbun ’yan siyasa da suka fito daga yankin, tare da yi musu gargadi da kakkausar murya.

Kungiyar ta NEF ta bukaci ‘yan Arewa da su kara taka tsan-tsan wajen kare hakkinsu, musamman a lokacin zabe, ta kuma yi gargadin cewa kada su fada cikin magudin shugabanni marasa kishin kasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp