Home General Sojojin Nijeriya sun kwato litar mai dubu 80 a yankin Niger Delta

Sojojin Nijeriya sun kwato litar mai dubu 80 a yankin Niger Delta

Sojojin Nijeriya sun sami nasarar kwato litar man fetur dubu 80 da aka sace a yankin Niger Delta.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mukaddashin mataimakin daraktan yada labaran rundunar sojin ta 6 Laftanar kanal Danjuma Jonah Danjuma ya fitar a ranar lahadi, wadda ta ce dakarun sojojin shiyya ta 6 sun gudnar da wani sumame a daga rabar 18 zuwa 24 ga watan Nuwamban 2024.

a wani bangare na kakkabe masu yin zagon kasa ga tattalin arzikin yankin na Niger delta dake da arzikin man fetur.

sanarwar ta ce a jihar Bayelsa dakarun sun gudanar da sumame masu tarin yawa wanda ya suka sami nasarori, inda a karamar hukumar Ekeremor suka kama wani jingin ruwan katako dake dauke da lita sama da dubu 2 da dari 5 da aka sato.

haka kuma a garin Sangakubu da ke karamar hukumar Nembe, dakarun sun sami nasarar bankado matatar mai da bata garin ke aiki da ita ba bisa kaida ba, dakarun sun fadada ayyukan zuwa karamar kudancin Ijaw a yankin Tebidaba Creek, in da suka kame wani jirgin ruwan dauke wasu ma’adanai da aka sata.

yayin sumamen, dakarun sojojin sun lalata matatun mai 34 da ake gudanar da su ba bisa ka’idaba, gami da kama mutane 11 da ake zargi da satar mai da kananan jiragen ruwa 19.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp