Home General Sojojin Nijeriya sun kwato litar mai dubu 80 a yankin Niger Delta

Sojojin Nijeriya sun kwato litar mai dubu 80 a yankin Niger Delta

Sojojin Nijeriya sun sami nasarar kwato litar man fetur dubu 80 da aka sace a yankin Niger Delta.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mukaddashin mataimakin daraktan yada labaran rundunar sojin ta 6 Laftanar kanal Danjuma Jonah Danjuma ya fitar a ranar lahadi, wadda ta ce dakarun sojojin shiyya ta 6 sun gudnar da wani sumame a daga rabar 18 zuwa 24 ga watan Nuwamban 2024.

a wani bangare na kakkabe masu yin zagon kasa ga tattalin arzikin yankin na Niger delta dake da arzikin man fetur.

sanarwar ta ce a jihar Bayelsa dakarun sun gudanar da sumame masu tarin yawa wanda ya suka sami nasarori, inda a karamar hukumar Ekeremor suka kama wani jingin ruwan katako dake dauke da lita sama da dubu 2 da dari 5 da aka sato.

haka kuma a garin Sangakubu da ke karamar hukumar Nembe, dakarun sun sami nasarar bankado matatar mai da bata garin ke aiki da ita ba bisa kaida ba, dakarun sun fadada ayyukan zuwa karamar kudancin Ijaw a yankin Tebidaba Creek, in da suka kame wani jirgin ruwan dauke wasu ma’adanai da aka sata.

yayin sumamen, dakarun sojojin sun lalata matatun mai 34 da ake gudanar da su ba bisa ka’idaba, gami da kama mutane 11 da ake zargi da satar mai da kananan jiragen ruwa 19.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp