Home General Sojojin Nijeriya sun kwato litar mai dubu 80 a yankin Niger Delta

Sojojin Nijeriya sun kwato litar mai dubu 80 a yankin Niger Delta

Sojojin Nijeriya sun sami nasarar kwato litar man fetur dubu 80 da aka sace a yankin Niger Delta.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mukaddashin mataimakin daraktan yada labaran rundunar sojin ta 6 Laftanar kanal Danjuma Jonah Danjuma ya fitar a ranar lahadi, wadda ta ce dakarun sojojin shiyya ta 6 sun gudnar da wani sumame a daga rabar 18 zuwa 24 ga watan Nuwamban 2024.

a wani bangare na kakkabe masu yin zagon kasa ga tattalin arzikin yankin na Niger delta dake da arzikin man fetur.

sanarwar ta ce a jihar Bayelsa dakarun sun gudanar da sumame masu tarin yawa wanda ya suka sami nasarori, inda a karamar hukumar Ekeremor suka kama wani jingin ruwan katako dake dauke da lita sama da dubu 2 da dari 5 da aka sato.

haka kuma a garin Sangakubu da ke karamar hukumar Nembe, dakarun sun sami nasarar bankado matatar mai da bata garin ke aiki da ita ba bisa kaida ba, dakarun sun fadada ayyukan zuwa karamar kudancin Ijaw a yankin Tebidaba Creek, in da suka kame wani jirgin ruwan dauke wasu ma’adanai da aka sata.

yayin sumamen, dakarun sojojin sun lalata matatun mai 34 da ake gudanar da su ba bisa ka’idaba, gami da kama mutane 11 da ake zargi da satar mai da kananan jiragen ruwa 19.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp