Home General Tattalin arziƙin Najeriya ya bunƙasa – NBS

Tattalin arziƙin Najeriya ya bunƙasa – NBS

Hukumar ƙididdiga ta ƙasa, wato NBS, ta ce tattalin arzikin Najeriya ya bunƙasa da kashi 3.46 a rubu’i na uku na wannan shekarar ta 2024.

Wannan nasarar ta samu ne a cikin sauri idan aka kwatanta da rubu’i biyu na farko a shekarar ta 2024, kamar yadda rahoton NBS ya nuna.

Sai dai duk da bunƙasar ta tattazlin arzikin, wato kashi 3.19 a rubu’i na biyu, da 2.98 a rubu’i na farko, har yanzu ba a kai ga samun nasarar bunƙasa tattalin arzikin ƙasar da kashi 6 ba kamar yadda gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ta yi alƙawari.

Nasarar da aka samu ba ta rasa nasaba da ci gaban da aka samu a ɓangaren harkokin tattalin arziki da suka shafi bankuna da intanet, wanda ya inganta tattalin arzikin ƙasar da kashi 50 a tsakanin Yuli da Satumba.

Wasu matakan da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya ɗauka a makonsa na farko a mulki sun sa an yi tunanin zai bunƙasa tare da inganta tattalin arzikin ƙasar, wada ita ce mafi girman tattalin arzikin nahiyar.

Amma bayan wata 18 da fara mulkin, manyan matakan da ya ɗauka – cire tallafin man fetur da karya darajar naira – sun jawo tsadar rayuwa da aka daɗe ba a gani ba a ƙasar a cikin shekaru masu yawa, amma har yanzu ba a fara gani a ƙasa ba.

Ɓangaren man fetur na ƙasar, wanda shi ne kan gaba wajen samar da kuɗin shiga ga gwamnatin ƙasar, ya samu bunƙasa da kashi 5.17, inda gangar man da ake fitarwa a ƙasar ya ƙaru zuwa ganga miliyan 1.47 a rana, maimakon ganga miliyan 1.41 da ake fitarwa a rubu’i na biyu na shekarar.

An samu koma-baya ne a ɓangaren noma daga kashi 1.41 a rubu’i na biyu, zuwa 1.14 a rubu’i na ukun, sannan ɓangaren masana’antu ya samu tagomashi daga 2.18 zuwa 3.35 a watan Afrilu zuwa Yuni.

Bankin bayar da lamuni ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Najeriya zai haɓaka da kashi 2.9 a shekarar 2024, da kuma 3.2 a shekara mai zuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp