Hukumar alhazan Kano ta nuna damuwa kan rashin sayen kujerun aikin Hajjin bana

Shugaban hukumar alhazan jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya nuna damuwarsa kan ƙarancin sayen kujerun aikin Hajji mai zuwa.

Shugaban ya bayyana hakan ne a yau Talata yayin wani taron haɗin gwiwa tsakanin ma’aikatan hukumar da da kuma manyan jami’anta na ƙananan hukumomi, a ofishin hukumar da ke Kano, kamar yadda wata sanarwa da kakakin hukumar Sulaiman A. Dederi ya fitar ta bayyana.

Alhaji Lamin ya buƙaci shugabannin hukumar na ƙananan hukumomi da su tashi haiƙan su ƙara azama wajen ganin an sayar da yawan kujerun da aka ware wa yankunansu.

Haka kuma ya yi kira da a samar da dabaru na bunƙasa cinikin kujerun da cimma aikin da ke gaban jihar a kan lokaci.

Hukumar alhazan ta sanya ranar 1 ga watan Janairu na shekara mai kamawa, 2025, a matsayin ranar rufe karɓar kuɗin ajiya na aikin Hajjin na bana daga maniyyata a jihar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 2 hours 16 minutes 26 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 3 hours 57 minutes 51 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com