Home General NNPCL na gudanar da jarrabawar ɗaukar ma’aikata

NNPCL na gudanar da jarrabawar ɗaukar ma’aikata

Babban kamfanin mai na Najeriya NNPCL na gudanar da jarrabawar ɗaukar sabbin ma’aikata.

Cikin wani saƙo da kamfanin ya wallafa a shafinsa na X, ya ce kimanin mutum 45,689 ne suke gudanar da jarrabawar wadda aka yi da kwamfuta.

”A yau NNPCL ya fara gudanar da jarrabawar ɗaukar ma’aikata da ake gudanarwa ta hanyar kwamfuta a cibiyoyi da dama a faɗin ƙasar nan”, in ji sanarwar.

NNPCL ya bayyana tsarin ɗaukar ma’aikatan da cewa tsari ne da yake gudanarwa a bayyane domin bai wa kowa dama.

”Domin damawa a kowa wajen ɗaukar aiki, NNPCL ya yi tanadi na musamman domin tabbatar da masu lalurar buƙata ta musamman da ke cikin masu neman aikin, sun samu damar gudanar da jarrabawar ba tare da wata matsala ba”, kamar yadda kamfanin ya wallafa a shafinsa na X

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp