Za mu biya kudaden daliban Kano da Ganduje ya gaza biya a Cyprus – Gwamna Abba

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya dauki matakin magance matsalolin da daliban Kano wadanda gwamnatin Ganduje ta tura karatu kuma suka kasa karbar shaidar kammala karatunsu.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria a ranar Litinin, ta bayyana cewa gwamna Yusuf ya yi wata muhimmiyar ganawa da mahukuntan jami’ar Near East da ke Cyprus domin shawo kan lamarin.

Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan batun bayar da satifiket ga daliban Kano da suka kammala karatunsu a shekarar 2015 zuwa 2019.

Da yawa daga cikin wadannan daliban da aka yaye, musamman wadanda suka yi karatu a fannonin aikin likitanci da aikin jinya, sun kasa samun damar yin aikin da suka koya, sakamakon gaza biyan kudin makaranta da gwamnatin Ganduje ta yi.

Gwamnan ya bayyana lamarin a matsayin babban koma-baya, ba wai ga daliban da abin ya shafa ba, har ma da jihar, wadda take da bukatar kwararru jami’an kula da lafiya.

Gwamnana Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnatinsa zata biya duk kudaden da ake bin daliban domin su karɓi Satifiket dinsu don su fara amfani da abun da suka koya domin amfanin al’umma.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 18 hours 45 minutes 6 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 20 hours 26 minutes 31 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com