Home General Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kula da gidajen yari

Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kula da gidajen yari

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya naɗa Nwakuche Ndidi, a matsayin shugaban riƙo na hukumar kula da gidajen yarin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da sakataren ma’aikatar hukumar tsaro ta sibil difens da hukumar kashe gobara da ta shige da fice, Ja’afaru Ahmed ya ce naɗin Ndidi zai fara aiki daga ranar 15 ga watan Disamba.

Naɗin nasa na zuwa ne bayan ƙarewar wa’adin shugaban hukumar na yanzu, Haliru Nababa.

A ranar 18 ga watan Fabrairu ne dai tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya naɗa Nababa a muƙamin.

An haifi Nwakuche Ndidi ranar 26 ga watan Nuwamban shekarar 1966 a garin Oguta na jihar Imo.

Kafin naɗinsa kan muƙamin shi ne mataimakin shugaban hukumar mai lura da horaswa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp