Home General Mene ya sa Gwamnonin Nijeriya ke butar ýan sandan Jiha

Mene ya sa Gwamnonin Nijeriya ke butar ýan sandan Jiha

Majalisar tattalin arzikin Najeriya (NEC) ta karɓi rahotonnin matsayar gwamnonin jihohin ƙasar 36 kan kafa rundunonin ‘yansandan jihohi.

Majalisar tattalin arzikin ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban ƙasa, ta yi zamanta a jiya Alhamis a fadar gwamnatin ƙasar da ke Abuja, inda gwamnoni da mataimakan wasu gwamnonin suka halarta tare da wasu masu bai wa shugaban ƙasa shawara.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai a fadar gwamnatin jim kaɗan bayan kammala ganawar, gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya ce gwamnonin jihohin sun nuna cikakken goyon bayansu kan ƙirƙirar ‘yansandan jihohi saboda matsalolin tsaro da jihohin ke fama da su.

“Tabbas kowace jiha na da irin nata matsalolin da suka shafi tsaro, kuma da dama sun amince da kafa rundunonin ‘yansandan jihohi a matsayin mafita kan matsalolin,” in ji gwamnan na Kaduna.

To sai da majalisar ta dakatar da tattaunawa game da batun har sai a zamanta na gaba da za a yi cikin watan Janairun sabuwar shekara mai kamawa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp