Gwamnan Kano ya saka sunan Sagagi cikin sabbin kwamishinoni Jihar

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya aikewa majalissar dokokin jihar wasika mai dauke da sunayen mutane 6 da yake son nadawa a matsayin kwamishinoni domin neman amincewa.

Idan za a iya tunawa a makon da ya wuce gwamnan ya yiwa majalisar zartarwarsa garanbawul tare da sallamar wasu daga cikin su.

Shugaban Majalisar Alhaji Jibril Ismail Falgore shi ne ya karanta wasikar a yayin zaman majalisar na yau.

Wadanda gwamnan ya aike da sunan su sun hadar

1- Alh. Shehu Wada Sagagi

2- Alh. Abdulkadir Abdulsalam (AG)

3- Ibrahim A. Waiya

4- Dr. Isma’il Danmaraya

5- Dr Ghaddafi Sani Shehu

6- Dr. Dahir M. Hashim.

Majalissar ta bukace su, su bayyana a gaban ta a gobe talata da misalin karfe goma na safe domin tantance su.

Ga dai sunayen ma’aikatun da a yanzu haka ba su da kwamishinoni:

1.  Hukumar raya karkara

2. Ma’aikatar Kudi

3. Muhalli

4. Yada Labarai

5. Jin kai

6. Makamashi

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1464 days 14 hours 44 minutes 27 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1446 days 16 hours 25 minutes 52 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com