Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya aikewa majalissar dokokin jihar wasika mai dauke da sunayen mutane 6 da yake son nadawa a matsayin kwamishinoni domin neman amincewa.
Idan za a iya tunawa a makon da ya wuce gwamnan ya yiwa majalisar zartarwarsa garanbawul tare da sallamar wasu daga cikin su.
Shugaban Majalisar Alhaji Jibril Ismail Falgore shi ne ya karanta wasikar a yayin zaman majalisar na yau.
Wadanda gwamnan ya aike da sunan su sun hadar
Read Also:
1- Alh. Shehu Wada Sagagi
2- Alh. Abdulkadir Abdulsalam (AG)
3- Ibrahim A. Waiya
4- Dr. Isma’il Danmaraya
5- Dr Ghaddafi Sani Shehu
6- Dr. Dahir M. Hashim.
Majalissar ta bukace su, su bayyana a gaban ta a gobe talata da misalin karfe goma na safe domin tantance su.
Ga dai sunayen ma’aikatun da a yanzu haka ba su da kwamishinoni:
1. Hukumar raya karkara
2. Ma’aikatar Kudi
3. Muhalli
4. Yada Labarai
5. Jin kai
6. Makamashi
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1488 days 23 hours 43 minutes 45 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1471 days 1 hour 25 minutes 10 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com