Sabuwar ƙungiyar matasan arewacin Najeriya ta LND ƙarkashin jagorancin shugabanta kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Ibrahim Shekarau, ta nemi a yi gyaran fuska ga sabon ƙudirin haraji mai cike da cece-kuce da shugaban ƙasar Bola Tinubu ya gabatarwa majalisar dokokin kasar.
Read Also:
Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a ranar Alhamis a Abuja a wajen gabatar da rahoton kwamitin kwararru da ta kafa domin yin nazari kan kudirin sake fasalin harajin da ya janyo cece-kuce a ƙasar.
Tun bayan gabatar da ƙudirin da shugaba Tinubu ya yi, na sake fasalin dokar haraji, ya haifar da zazzafar muhawara a fadin ƙasar, masamman masu fada a ji a yankin arewacin ƙasar da ke zargin zai haifar da koma baya ga yankin.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1464 days 19 hours 44 minutes 18 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1446 days 21 hours 25 minutes 43 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com