Home General Dangote za ta haɗa kai da kamfanin MRS don sayar da litar...

Dangote za ta haɗa kai da kamfanin MRS don sayar da litar fetur naira 935

Matatar mai ta Dangote a Najeriya ta ce za ta haɗa hannu da kamfanin mai na MRS domin sayar da litar man fetur a kan kuɗi naira 935 a gidajen mansa da ke faɗin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da kamfanin Dangoten ya fitar ranar Asabar, ya ce shugaban kamfanin Aliko Dangote ya yaba wa shugaban Najeriya Bola Tinbu kan matakin da ya ɗauka na sayar wa matatarsa ɗanyen mai da kuɗin naira, wanda ya ce ya yi tasiri kan tattalin arzikin ƙasar.

Dangote ya ce hakan ya kuma taimaka wajen samun raguwar kuɗin man fetur a cikin ƙasar.

“Domin kawo wa ‘yan Najeriya sauƙi, a baya Dangote ya rage farashin mai daga 970 zuwa 899.50 ga masu sarin man a matatarsa, kuma domin tabbatar da ragin ya isa kan masu amfani da man, mun cimma yarjejeniya da kamfanin MRS domin sayar da man kan naira 935 a gidanjen mansa,” kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

Matakin na zuwa ne bayan da babban kamfanin mai na ƙasar NNPCL ya sanar da rage farashin man zuwa ƙasa da naira 1,000.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp