Gwamnatin tarayya ta bayar da hutun aiki a ranar Laraba 25 da Alhamis 26 ga watan Disamban 2024 domin bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara.
Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da babban sakatariyar ma’aikatan, Magdalene Ajani, ta fitar a ranar Litinin.
Read Also:
- Rahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara Ne
- Pantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama’a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a Gombe
- Ma’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’
Tunji-Ojo ya miƙa gaisuwarsa ga ƴan Najeriya, sannan ya yi kira gare su yi amfani da lokacin bukuwan domin nuna ƙauna da kira ga zaman lafiya.
Ya ce gwamnatin Najeriya a shirye take ta cigaba da tabbatar da zaman lafiya da tsaro da ci gaban ƙasar, sannan ya taya kiristoci murna, tare da musu fatan alheri.












