Gwamnatin tarayya ta bayar da hutun aiki a ranar Laraba 25 da Alhamis 26 ga watan Disamban 2024 domin bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara.
Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da babban sakatariyar ma’aikatan, Magdalene Ajani, ta fitar a ranar Litinin.
Read Also:
- Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar Shekara
- Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci
- Binciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?
Tunji-Ojo ya miƙa gaisuwarsa ga ƴan Najeriya, sannan ya yi kira gare su yi amfani da lokacin bukuwan domin nuna ƙauna da kira ga zaman lafiya.
Ya ce gwamnatin Najeriya a shirye take ta cigaba da tabbatar da zaman lafiya da tsaro da ci gaban ƙasar, sannan ya taya kiristoci murna, tare da musu fatan alheri.












