Home General Dangote za ta haɗa kai da kamfanin MRS don sayar da litar...

Dangote za ta haɗa kai da kamfanin MRS don sayar da litar fetur naira 935

Matatar mai ta Dangote a Najeriya ta ce za ta haɗa hannu da kamfanin mai na MRS domin sayar da litar man fetur a kan kuɗi naira 935 a gidajen mansa da ke faɗin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da kamfanin Dangoten ya fitar ranar Asabar, ya ce shugaban kamfanin Aliko Dangote ya yaba wa shugaban Najeriya Bola Tinbu kan matakin da ya ɗauka na sayar wa matatarsa ɗanyen mai da kuɗin naira, wanda ya ce ya yi tasiri kan tattalin arzikin ƙasar.

Dangote ya ce hakan ya kuma taimaka wajen samun raguwar kuɗin man fetur a cikin ƙasar.

“Domin kawo wa ‘yan Najeriya sauƙi, a baya Dangote ya rage farashin mai daga 970 zuwa 899.50 ga masu sarin man a matatarsa, kuma domin tabbatar da ragin ya isa kan masu amfani da man, mun cimma yarjejeniya da kamfanin MRS domin sayar da man kan naira 935 a gidanjen mansa,” kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

Matakin na zuwa ne bayan da babban kamfanin mai na ƙasar NNPCL ya sanar da rage farashin man zuwa ƙasa da naira 1,000.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a Jihar
X whatsapp