Home General PDP ta dora alhakin talaucin da ‘ya Nijeriya suke ciki kan APC

PDP ta dora alhakin talaucin da ‘ya Nijeriya suke ciki kan APC

Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya, PDP, ta ce turmutsutsun da aka samu a Najeriya guda uku cikin ƙanƙanin lokaci ya nuna cewa akwai talauci da yunwa a ƙasar, wanda a cewarta yana da nasaba da irin mulkin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu.

Kakakin PDP na ƙasa, Debo Ologunagba ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da tashar Channels ta ruwaito, inda ya ce turmutsutsun da ake samu wajen rabon abinci abu ne da za a iya kiyaye aukuwarsu.

“PDP na baƙin ciki yadda gwamnatin APC te ɗaiɗaita tattalin arzikin ƙasar nan tare da jefa miliyoyin mutane cikin ƙangin talauci da yunwa, inda mutane da dama ba sa iya cin abinci, har wasu suke gwammace tafiya ƙasashen waje suna aiki masu wahala.

“Akwai takaici ganin duk da ɗimbin arzikin da Najeriya ke da shi, ƴan ƙasar suna rayuwa cikin ƙunci, har ta kai suna mutuwa wajen karɓar abinci.

PDP ta kuma yi kira ga gwamnatin ta sake duba matakan da ta ɗauka da suka jawo tsadar rayuwa a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp