Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya, PDP, ta ce turmutsutsun da aka samu a Najeriya guda uku cikin ƙanƙanin lokaci ya nuna cewa akwai talauci da yunwa a ƙasar, wanda a cewarta yana da nasaba da irin mulkin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu.
Kakakin PDP na ƙasa, Debo Ologunagba ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da tashar Channels ta ruwaito, inda ya ce turmutsutsun da ake samu wajen rabon abinci abu ne da za a iya kiyaye aukuwarsu.
Read Also:
- Rahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara Ne
- Pantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama’a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a Gombe
- Ma’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’
“PDP na baƙin ciki yadda gwamnatin APC te ɗaiɗaita tattalin arzikin ƙasar nan tare da jefa miliyoyin mutane cikin ƙangin talauci da yunwa, inda mutane da dama ba sa iya cin abinci, har wasu suke gwammace tafiya ƙasashen waje suna aiki masu wahala.
“Akwai takaici ganin duk da ɗimbin arzikin da Najeriya ke da shi, ƴan ƙasar suna rayuwa cikin ƙunci, har ta kai suna mutuwa wajen karɓar abinci.
PDP ta kuma yi kira ga gwamnatin ta sake duba matakan da ta ɗauka da suka jawo tsadar rayuwa a ƙasar.












