Sanata mai wakiltar Borno ta Kudu, Mohammed Ali Ndume, ya ce yankin arewa ba cima-zaune ba ne idan ana maganar tattalin arziki.
Ndume ya bayyana haka ne a wata sanarwa, inda ya ce kowace jiha ko yanki da ke ƙasar na buƙatar wani domin ci gaba, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Read Also:
- Rahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara Ne
- Pantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama’a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a Gombe
- Ma’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’
Sanatan ya ce, “yankin Arewa ba zai taɓa zama cima-zaune ba ko mai dogaro da wani yankin saboda muna da arziki.
“Waɗanda suke tunanin wai waɗannan ƙudurorin harajin arewa zai shafa, ba su fahimta ba ne. Dukkan wani mai ƙaramin samu a ƙasar sai lamarin ya shafe shi.”












