Home General CISLAC ta yi gargaɗi kan cushe a kasafin kuɗin 2025

CISLAC ta yi gargaɗi kan cushe a kasafin kuɗin 2025

Cibiyar rajin kyautata ayyukan majalisar dokoki da yaƙi da rashawa a Najeriyar wato CISLAC, ta yi kira da a guji yin cushe a kasafin kuɗin 2025, tare da kira ga gwamnatin tarayya ta tabbatar da kasafta kuɗaɗe kan abubuwan da ƴan ƙasar ke buƙata.

A wata sanarwa da shugaban cibiyar, Auwal Ibrahim Musa (Rafsanjani), ya fitar, CISLAC ta ce cushe a kasafin kuɗi da kasafta kuɗaɗe masu yawa a ayyukan da ba su cancanta ba, bai dace ba, inda ya yi misali da kasafta wa ma’aikatar wasanni da ta Neja Delta kuɗaɗe waɗanda an riga an rufe su.

Da take amfani da rahoton babban mai binciken kuɗi na bana, CISLAC ta bayyana wasu kuɗaɗe da aka cire da suka sha banbam, inda ta ce an cire sama da naira biliyan 197.72 domin wasu ayyuka a ma’aikatu tsakanin 2020 da 2021 ba bisa ƙa’ida ba.

Cibiyar sai ta yi kira ga majalisar da ta yi nazarin kasafin kuɗin cikin mutunci da nagarta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a Jihar
X whatsapp