Home General Yadda Gwamnan Adamawa ya kirkiri sabbin Masarautu bakwai a jihar

Yadda Gwamnan Adamawa ya kirkiri sabbin Masarautu bakwai a jihar

Gwamnan Jihar Adamawa da ke arewa maso gabashin Najeriya, Ahmadu Umaru Fintiri ya sanar da ƙirƙiro sabbin masarautu bakwai a jihar.

Sabbin masarutun sun haɗa da masarautar Huba da ke Hong, da masarautar Madagali da ke Gulak, da masarautar Michika da ke Michika da masarautar Fufore da ke Fufore da masarautar Gombi da ke Gombi, da masarautar Yungur da ke Dumne, sai kuma masarautar Maiha da ke Maiha.

A cewar gwamnan, masarautar Huba da Madagali da Michika da kuma Fufore na da matakin girma na biyu, yayin da masarautun Gombi da na Yungur da kuma na Maiha an basu matakin girma na uku.

”ƙirƙiro waɗannan sabbin masarautun na da nufin inganta matsayin masarautu wajen samar da zaman lafiya da tsaro da kuma cigaban jihar,” a cewar gwamnan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp