Home General Ba na danasanin cire Tallafin Man fetur – Tinubu

Ba na danasanin cire Tallafin Man fetur – Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya ce ba ya nadamar cire tallafin man fetur da ya yi a farkon kama mulkinsa.

Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Litinin da daddare, a tattaunawarsa ta farko da kafafen yaɗa labaru tun bayan hawa mulkin Najeriya a watan Mayun 2023.

Shugaban na Najeriya ya bayyana hakan ne a lokacin da aka yi masa tambaya kan ‘ko da ya fi kyau idan an jinkirta cire tallafin man fetur da kuma barin kasuwa ta tantance darajar naira’.

Tinubu ya ce “babu yadda za a yi na bari ana sayar da man fetur ta yadda ƙasashe maƙwafta za su riƙa samun garaɓasa. Ba na nadamar komai game da cire tallafin man fetur.

”Muna kashe abin da za mu amfana da shi a gaba ne, muna yaudarar kanmu ne kawai, wannan sauyi dole ne, ” in ji shi.

Sannan ya kara da cewa shi ko alama bai yarda da tsarin kayyade farashi ba kuma ba zai yi hakan ba, illa dai za su yi aiki tukuru su tabbatar sun samar da man a kasuwa.

A ranar 29 ga watan Mayun 2023, lokacin jawabin karɓar mulki ne Bola Tinubu ya bayyana cire tallafin man fetur.

Masana da dama na kallon cire tallafin man fetur da barin kasuwa ta tantance darajar naira a matsayin abubuwan da suka ta’azzara matsalar tattalin arziƙi da al’ummar ƙasar suka faɗa ciki.

Tun bayan cire tallafin farashin man daga kusan naira 200 a kan lita daya zuwa sama da naira dubu daya abubuwa suka ta’azzara ga ‘yan kasar kasancewar man ya damfara ga yawancin harkokin rayuwar al’ummar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp