Home General Ba na danasanin cire Tallafin Man fetur – Tinubu

Ba na danasanin cire Tallafin Man fetur – Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya ce ba ya nadamar cire tallafin man fetur da ya yi a farkon kama mulkinsa.

Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Litinin da daddare, a tattaunawarsa ta farko da kafafen yaɗa labaru tun bayan hawa mulkin Najeriya a watan Mayun 2023.

Shugaban na Najeriya ya bayyana hakan ne a lokacin da aka yi masa tambaya kan ‘ko da ya fi kyau idan an jinkirta cire tallafin man fetur da kuma barin kasuwa ta tantance darajar naira’.

Tinubu ya ce “babu yadda za a yi na bari ana sayar da man fetur ta yadda ƙasashe maƙwafta za su riƙa samun garaɓasa. Ba na nadamar komai game da cire tallafin man fetur.

”Muna kashe abin da za mu amfana da shi a gaba ne, muna yaudarar kanmu ne kawai, wannan sauyi dole ne, ” in ji shi.

Sannan ya kara da cewa shi ko alama bai yarda da tsarin kayyade farashi ba kuma ba zai yi hakan ba, illa dai za su yi aiki tukuru su tabbatar sun samar da man a kasuwa.

A ranar 29 ga watan Mayun 2023, lokacin jawabin karɓar mulki ne Bola Tinubu ya bayyana cire tallafin man fetur.

Masana da dama na kallon cire tallafin man fetur da barin kasuwa ta tantance darajar naira a matsayin abubuwan da suka ta’azzara matsalar tattalin arziƙi da al’ummar ƙasar suka faɗa ciki.

Tun bayan cire tallafin farashin man daga kusan naira 200 a kan lita daya zuwa sama da naira dubu daya abubuwa suka ta’azzara ga ‘yan kasar kasancewar man ya damfara ga yawancin harkokin rayuwar al’ummar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar NejaMiyagun ƙwayoyi da Makamai: Jami'an Tsaro Sun Kama Mutane 8 a Jihar YobeAbin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto
X whatsapp