Home General CISLAC ta yi gargaɗi kan cushe a kasafin kuɗin 2025

CISLAC ta yi gargaɗi kan cushe a kasafin kuɗin 2025

Cibiyar rajin kyautata ayyukan majalisar dokoki da yaƙi da rashawa a Najeriyar wato CISLAC, ta yi kira da a guji yin cushe a kasafin kuɗin 2025, tare da kira ga gwamnatin tarayya ta tabbatar da kasafta kuɗaɗe kan abubuwan da ƴan ƙasar ke buƙata.

A wata sanarwa da shugaban cibiyar, Auwal Ibrahim Musa (Rafsanjani), ya fitar, CISLAC ta ce cushe a kasafin kuɗi da kasafta kuɗaɗe masu yawa a ayyukan da ba su cancanta ba, bai dace ba, inda ya yi misali da kasafta wa ma’aikatar wasanni da ta Neja Delta kuɗaɗe waɗanda an riga an rufe su.

Da take amfani da rahoton babban mai binciken kuɗi na bana, CISLAC ta bayyana wasu kuɗaɗe da aka cire da suka sha banbam, inda ta ce an cire sama da naira biliyan 197.72 domin wasu ayyuka a ma’aikatu tsakanin 2020 da 2021 ba bisa ƙa’ida ba.

Cibiyar sai ta yi kira ga majalisar da ta yi nazarin kasafin kuɗin cikin mutunci da nagarta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp