Home General Gwamnati Ta Tashi Kasuwar Kwanar Gafan dake Garun Malam a Kano

Gwamnati Ta Tashi Kasuwar Kwanar Gafan dake Garun Malam a Kano

Majalisar karamar hukumar Garun mallam a jihar Kano, ta baiwa mazauna kasuwar Kwanar Gafan wa’adin kwana bakwai da su tashi daga cikin kasuwar har zuwa wani lokaci nan gaba.

Shugaban karamar hukumar, Barr. Aminu Salisu Kadawa ne ya bada umarnin hakan a wajen bikin kaddamar da sake fasalin farfado da tattalin arzikin yankin.

Kadawa ya ce “Duba da yadda aka mai da kasuwar tamkar wata mafaka da cibiyar yada badala maimakon ainihin yin abun da yasa aka kafa kasuwar tun farko, amma Mun fahimci kasuwar ta sauka daga Kan Manufar da tasa aka samar da ita. Ya bukaci mazauna kasuwar da su tattara kayansu su bar wajen, tun kafin ranar 1 ga watan Janairu 2025, idan ba haka ba duk wanda aka kama za a hukunta shi.

” Nan gaba Kadan za mu bayyana lokacin da za a yi bikin sake bude kasuwar don cigaba da kasuwancin iri daban-daban ba ma na kayan Gona ba har nau’in sauran ababan more rayuwa don inganta tattalin arzikin yankin”. Barr Aminu Salisu

Ya bukaci yan kasuwa da zo domin saka jarinsu a kasuwar, domin za a gyara kasuwar ta yadda zata yi dai-dai da zamani.

Wani malamin addinin islama, Imam Abdullahi Yusif Chiromawa, ya bayyana cewa kasuwar Kwanar Gafan ta zama barazana ga tarbiyar yaransu, ya ce abubunwan da Ake a kasuwar ya sabawa shari’ar musulunci.

Malam Abdullah ya ce Kasuwar ta zama wajen aikata zinace-zinace ,Luwadi, da madigo ga matasa da kuma kawo matan aure, Sannan kuma mafaka ce ga Barayi da yan fashi da masu safarar mugagga kwayoyi, don haka ya gode shugaban karamar hukumar bisa namijin kokarin da ya nuna don kaucewa kara fadawa cikin fushi Allah.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp