Home General Akwai yiwuwar ƙara kuɗin kira da na data a sabuwar shekarar 2025...

Akwai yiwuwar ƙara kuɗin kira da na data a sabuwar shekarar 2025 a Najeriya

Akwai yuwuwar kamfanonin sadarwa a Najeriya su samu amincewar hukumar da ke kula da su NCC domin su ƙara kuɗin data da na kiran waya a sabuwar shekarar 2025.

Wani babban jami’i da ya nemi a sakaya sunanshi ya ce hukumar sadarwa ta Najeriya NCC ka iya bai wa kamfanonin damar ƙara kuɗi.

Dailytrust ta rawaito cewa dukda tsadar rayuwa ammaanƙi amincewa kamfanonin su ƙara kuɗin kira sama da shekaru 11 da suka gabata.

Kamfanoni kamar MTN da Airtel da 9Mobile sun jima suna miƙa buƙatar ƙarin kuɗin GA Hukumar duba da yanayin tattalin arziki a ƙasar.

Wasu majiyoyin kamfanonin sadarwar sun ce ƙarin da za a fuskanta a ƙasar zai iya kaiwa kaso 40.

Wannan na nufin cewa kiran waya na minti 1 zai tashi daga naira 11 zuwa 15.40, aika sakon kar ta kwana a salula zai tashi daga naira 4 zuwa naira 5.60.

Farashin data 1GB zai tashi daga naira dubu 1 zuwa dubu1 da 400

A ranar 20 ga watan disamba a wata tattaunawa da manema labarai ministan sadarwa na Najeriya Dr. Bosun Tijani ya nuna cewar akwai buƙatar sake duba farashin.

A shekarar 2023 ne kamfanin MTN yayi asarar da ta kai Naira biliyan 137, asarar da ta ƙaru zuwa biliyan 514.9 a watanni 9 na farkon 2024.

Kamfanin Airtel dake aiki a Afrika shima ya sanar da yin asarar da ta kai dala miliyan 89 a 2024 kuma hakan ya biyo ƙaluabalen da yake fuskanta a Najeriya

Kawo lokacin haɗa wannan rahoto babu wani martani daga hukumomin da abin ya shafa a Najeriya

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp