Home General Akwai yiwuwar ƙara kuɗin kira da na data a sabuwar shekarar 2025...

Akwai yiwuwar ƙara kuɗin kira da na data a sabuwar shekarar 2025 a Najeriya

Akwai yuwuwar kamfanonin sadarwa a Najeriya su samu amincewar hukumar da ke kula da su NCC domin su ƙara kuɗin data da na kiran waya a sabuwar shekarar 2025.

Wani babban jami’i da ya nemi a sakaya sunanshi ya ce hukumar sadarwa ta Najeriya NCC ka iya bai wa kamfanonin damar ƙara kuɗi.

Dailytrust ta rawaito cewa dukda tsadar rayuwa ammaanƙi amincewa kamfanonin su ƙara kuɗin kira sama da shekaru 11 da suka gabata.

Kamfanoni kamar MTN da Airtel da 9Mobile sun jima suna miƙa buƙatar ƙarin kuɗin GA Hukumar duba da yanayin tattalin arziki a ƙasar.

Wasu majiyoyin kamfanonin sadarwar sun ce ƙarin da za a fuskanta a ƙasar zai iya kaiwa kaso 40.

Wannan na nufin cewa kiran waya na minti 1 zai tashi daga naira 11 zuwa 15.40, aika sakon kar ta kwana a salula zai tashi daga naira 4 zuwa naira 5.60.

Farashin data 1GB zai tashi daga naira dubu 1 zuwa dubu1 da 400

A ranar 20 ga watan disamba a wata tattaunawa da manema labarai ministan sadarwa na Najeriya Dr. Bosun Tijani ya nuna cewar akwai buƙatar sake duba farashin.

A shekarar 2023 ne kamfanin MTN yayi asarar da ta kai Naira biliyan 137, asarar da ta ƙaru zuwa biliyan 514.9 a watanni 9 na farkon 2024.

Kamfanin Airtel dake aiki a Afrika shima ya sanar da yin asarar da ta kai dala miliyan 89 a 2024 kuma hakan ya biyo ƙaluabalen da yake fuskanta a Najeriya

Kawo lokacin haɗa wannan rahoto babu wani martani daga hukumomin da abin ya shafa a Najeriya

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp