Home General Gwamnati Ta Tashi Kasuwar Kwanar Gafan dake Garun Malam a Kano

Gwamnati Ta Tashi Kasuwar Kwanar Gafan dake Garun Malam a Kano

Majalisar karamar hukumar Garun mallam a jihar Kano, ta baiwa mazauna kasuwar Kwanar Gafan wa’adin kwana bakwai da su tashi daga cikin kasuwar har zuwa wani lokaci nan gaba.

Shugaban karamar hukumar, Barr. Aminu Salisu Kadawa ne ya bada umarnin hakan a wajen bikin kaddamar da sake fasalin farfado da tattalin arzikin yankin.

Kadawa ya ce “Duba da yadda aka mai da kasuwar tamkar wata mafaka da cibiyar yada badala maimakon ainihin yin abun da yasa aka kafa kasuwar tun farko, amma Mun fahimci kasuwar ta sauka daga Kan Manufar da tasa aka samar da ita. Ya bukaci mazauna kasuwar da su tattara kayansu su bar wajen, tun kafin ranar 1 ga watan Janairu 2025, idan ba haka ba duk wanda aka kama za a hukunta shi.

” Nan gaba Kadan za mu bayyana lokacin da za a yi bikin sake bude kasuwar don cigaba da kasuwancin iri daban-daban ba ma na kayan Gona ba har nau’in sauran ababan more rayuwa don inganta tattalin arzikin yankin”. Barr Aminu Salisu

Ya bukaci yan kasuwa da zo domin saka jarinsu a kasuwar, domin za a gyara kasuwar ta yadda zata yi dai-dai da zamani.

Wani malamin addinin islama, Imam Abdullahi Yusif Chiromawa, ya bayyana cewa kasuwar Kwanar Gafan ta zama barazana ga tarbiyar yaransu, ya ce abubunwan da Ake a kasuwar ya sabawa shari’ar musulunci.

Malam Abdullah ya ce Kasuwar ta zama wajen aikata zinace-zinace ,Luwadi, da madigo ga matasa da kuma kawo matan aure, Sannan kuma mafaka ce ga Barayi da yan fashi da masu safarar mugagga kwayoyi, don haka ya gode shugaban karamar hukumar bisa namijin kokarin da ya nuna don kaucewa kara fadawa cikin fushi Allah.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp