Home General Gwamnati Ta Tashi Kasuwar Kwanar Gafan dake Garun Malam a Kano

Gwamnati Ta Tashi Kasuwar Kwanar Gafan dake Garun Malam a Kano

Majalisar karamar hukumar Garun mallam a jihar Kano, ta baiwa mazauna kasuwar Kwanar Gafan wa’adin kwana bakwai da su tashi daga cikin kasuwar har zuwa wani lokaci nan gaba.

Shugaban karamar hukumar, Barr. Aminu Salisu Kadawa ne ya bada umarnin hakan a wajen bikin kaddamar da sake fasalin farfado da tattalin arzikin yankin.

Kadawa ya ce “Duba da yadda aka mai da kasuwar tamkar wata mafaka da cibiyar yada badala maimakon ainihin yin abun da yasa aka kafa kasuwar tun farko, amma Mun fahimci kasuwar ta sauka daga Kan Manufar da tasa aka samar da ita. Ya bukaci mazauna kasuwar da su tattara kayansu su bar wajen, tun kafin ranar 1 ga watan Janairu 2025, idan ba haka ba duk wanda aka kama za a hukunta shi.

” Nan gaba Kadan za mu bayyana lokacin da za a yi bikin sake bude kasuwar don cigaba da kasuwancin iri daban-daban ba ma na kayan Gona ba har nau’in sauran ababan more rayuwa don inganta tattalin arzikin yankin”. Barr Aminu Salisu

Ya bukaci yan kasuwa da zo domin saka jarinsu a kasuwar, domin za a gyara kasuwar ta yadda zata yi dai-dai da zamani.

Wani malamin addinin islama, Imam Abdullahi Yusif Chiromawa, ya bayyana cewa kasuwar Kwanar Gafan ta zama barazana ga tarbiyar yaransu, ya ce abubunwan da Ake a kasuwar ya sabawa shari’ar musulunci.

Malam Abdullah ya ce Kasuwar ta zama wajen aikata zinace-zinace ,Luwadi, da madigo ga matasa da kuma kawo matan aure, Sannan kuma mafaka ce ga Barayi da yan fashi da masu safarar mugagga kwayoyi, don haka ya gode shugaban karamar hukumar bisa namijin kokarin da ya nuna don kaucewa kara fadawa cikin fushi Allah.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp