Home General Gwamnati Ta Tashi Kasuwar Kwanar Gafan dake Garun Malam a Kano

Gwamnati Ta Tashi Kasuwar Kwanar Gafan dake Garun Malam a Kano

Majalisar karamar hukumar Garun mallam a jihar Kano, ta baiwa mazauna kasuwar Kwanar Gafan wa’adin kwana bakwai da su tashi daga cikin kasuwar har zuwa wani lokaci nan gaba.

Shugaban karamar hukumar, Barr. Aminu Salisu Kadawa ne ya bada umarnin hakan a wajen bikin kaddamar da sake fasalin farfado da tattalin arzikin yankin.

Kadawa ya ce “Duba da yadda aka mai da kasuwar tamkar wata mafaka da cibiyar yada badala maimakon ainihin yin abun da yasa aka kafa kasuwar tun farko, amma Mun fahimci kasuwar ta sauka daga Kan Manufar da tasa aka samar da ita. Ya bukaci mazauna kasuwar da su tattara kayansu su bar wajen, tun kafin ranar 1 ga watan Janairu 2025, idan ba haka ba duk wanda aka kama za a hukunta shi.

” Nan gaba Kadan za mu bayyana lokacin da za a yi bikin sake bude kasuwar don cigaba da kasuwancin iri daban-daban ba ma na kayan Gona ba har nau’in sauran ababan more rayuwa don inganta tattalin arzikin yankin”. Barr Aminu Salisu

Ya bukaci yan kasuwa da zo domin saka jarinsu a kasuwar, domin za a gyara kasuwar ta yadda zata yi dai-dai da zamani.

Wani malamin addinin islama, Imam Abdullahi Yusif Chiromawa, ya bayyana cewa kasuwar Kwanar Gafan ta zama barazana ga tarbiyar yaransu, ya ce abubunwan da Ake a kasuwar ya sabawa shari’ar musulunci.

Malam Abdullah ya ce Kasuwar ta zama wajen aikata zinace-zinace ,Luwadi, da madigo ga matasa da kuma kawo matan aure, Sannan kuma mafaka ce ga Barayi da yan fashi da masu safarar mugagga kwayoyi, don haka ya gode shugaban karamar hukumar bisa namijin kokarin da ya nuna don kaucewa kara fadawa cikin fushi Allah.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp